China ta kori wakilan majalisar dokokin kasar su uku wadanda aikin su yake da nasaba da sashen tsaro, kamar yadda kafofin yada labaran kasar suka bayyana a dai dai lokacin da ake binciken wani babban hafsan kasar, kuma lokacin da hukumomin kasar a Beijing suke daukar matakan sabunta dakarunta.
A sanarwar da kamfanin dillancin labaran kasar Xinhua ya bayar, bai bada dalilan da suka sa aka kori wakilan majalisar ba, ko rahoton ana gudanar da bincike akan su ba.
Gwamnatin lardi wacce take da iko kan yankunan da ‘yan majalisar uku suka fito, bata bada wani karin bayani ba da aka tuntube ta.
A halinda ake ciki kuma, kasar Girka ta kama wani jami’in sojan kasar kan zargin leken asiri, ana zargin yana da alaka da kasar China.


