Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta Afrika
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika

Gombe Ta Yi Kira Ga Jami’o’i Su Tallafa Wa Gwamnati Ta Hanyar Bincike Da Ƙirƙire-ƙirƙire
Published: July 7, 2026 at 5:02 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Gombe ta yi kira ga jami’o’i da sauran manyan makarantun gaba da sakandare da su ƙara taka rawar gani wajen magance matsalolin al’ummomin da suke ciki tare da tallafa wa gwamnati ta hanyar bincike da kirkire-kirkire.

Mataimakin Gwamnan jihar Gombe, Manassah Daniel Jatau, ne ya bayyana hakan yayin da ya karɓi tawagar shugabannin Jewel University ƙarƙashin jagorancin Mataimakin Shugaban Jami’ar, Yahya Ibrahim Yero, a ziyarar girmamawa da suka kai masa.

Dr. Jatau ya ce ya kamata jami’o’i su gina haɗin gwiwa na dabaru domin samun ɗorewar kuɗaɗen gudanarwa, su tabbatar da ingancin ilimi, sannan su yi amfani da kafafen yaɗa labarai wajen bayyana shirye-shiryensu da nasarorin da suke samu. Ya ƙara da cewa babu wata jami’a da za ta bunƙasa idan ta ware kanta daga al’ummar da take ciki.

Ya kuma bayyana cewa jihar Gombe yanzu tana da jami’o’i biyar, lamarin da ya ce babban ci gaba ne a fannin ilimi. Haka kuma ya buƙaci jami’ar ta haɗa kai da gwamnatin jihar wajen fuskantar matsalolin tsaro.

Mataimakin gwamnan ya kuma bayyana cewa ana shirin gudanar da bukukuwan cika shekaru 30 da ƙirƙirar Jihar Gombe, inda ya gayyaci jami’ar da ta ba da gudummawa ta hanyar bincike da shawarwarin masana domin tabbatar da nasarar bikin.

Dr. Jatau ya tabbatar wa jami’ar da ci gaba da samun goyon bayan gwamnatin jihar, tare da ƙarfafa gwiwar shugabanninta su ci gaba da tuntuɓar gwamnati idan akwai buƙatar taimako a hukumance.

Tun da farko, Mataimakin Shugaban Jewel University, Farfesa Yahya Ibrahim Yero, ya ce manufar ziyarar ita ce ƙarfafa haɗin gwiwa da gwamnatin jihar.

Ya bayyana cewa jami’ar na gudanar da shirye-shiryen karatu guda 25 da National Universities Commission ta amince da su.

Haka kuma ya bayyana cewa wanda ya kafa jami’ar ya samar da guraben karatu ga ɗalibai marasa galihu, musamman ‘yan asalin Jihar Gombe da sauran ɗaliban yankin Arewa maso Gabas.

Farfesa Yero ya sake jaddada kudirin jami’ar na samar da waɗanda suka kammala karatu masu ilimi, ƙwarewa da kyawawan ɗabi’u domin ba da gudummawa ga ci gaban ƙasa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Sabuwar Dama Ga Masu Zaɓe: INEC Ta Tsawaita CVR Zuwa Ƙarshen Yuli
Next Post: Sarakunan Gombe Da Zazzau Sun Yi Kira Ga ‘Yan Najeriya Su Rungumi Haɗin Kai Da Zaman Lafiya

Karin Labarai Masu Alaka

Ghana Ta Haramta Hakar Ma’adinai A Gandunan Dajin Data Kebe, Labarai
Cutar Kurkunu Ta Kusa Zamowa Tarihi A Duniya Amurka
Hawan Durba A Fadar Sarkin Zazzau Afrika
Kasar Iran Zata Kai Hare Haren Ramuwar Gayya Isra’ila Afrika
Iran Zata Kawo Karshen Yaki Da Isra’ila Da Amurka Amurka
An Kama Masu Fasa Kaurin Gawayi A Malawi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Trump Ya Bukaci Kasar Iran Ta Mika Wuya Amurka
  • Rundunar Hadinkan Saudiya Tayi Ikirarin Mayar Da Martani Ga ‘Yan Aware Labarai
  • Kotu A Abuja Tabawa Goodluck Jonathan Daman Tsayawa Takara Afrika
  • Prime Ministan Pakistan Yace Zai Karbi Bakoncin Tattaunawar Amurka Da Iran Afrika
  • Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
  • Shugabar Hamayya A Venezuela Ta Gana Da Paparoma Leo Amurka
  • Hukumar Zabe Ta Saukaka Gudanar Da Rijistar Katin Zabe A Najeriya Labarai
  • Amurka Ta Gabatarwa Sassan Dake Yakar Juna A Sudan da Shirin Tsagaita Wuta Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.