Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sanda, Sojoji Da DSS Sun Ceto ‘Yan NYSC Da Aka Sace A Kogi Afrika
  • Rundunar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Al’umma Su Kiyaye Doka Yayin Bikin Takutaha Afrika
  • RUWASSA Ta Hada Masu Ruwa Da Tsaki Domin Inganta Aiwatar Da Shirin NG-SURWASH Afrika
  • Rundunar ’Yan Sandan Bauchi Ta Kama Dattijo Kan Zargin Cin Zarafin Yarinya ’Yar Shekara 8 Afrika
  • Damara Ya Tallafa Wa Gasar Karatun Al-Qur’ani Da Naira Miliyan Biyar A Bambam Afrika

Gwamnan Bauchi Ya Shiga Neman Mafita Kan Lalacewar Matatar Ruwan Alkaleri
Published: August 30, 2026 at 1:26 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Bauchi a Arewa Maso Gabashin Najeriya Sanata Bala Abdulkadir Mohammed, ya gana da Shugaban Kamfanin Hummels Water Engineering na ƙasar Hungary, Injiniya Peter Hummel, a Abuja, domin nemo mafita kan matsalar matatar ruwan Alkaleri.

Ganawar ta biyo bayan bukatar Gwamna Bala Mohammed ga injiniyoyin Hungary da suka girka matatar, da su dawo Jihar Bauchi domin gudanar da gyare-gyare da aikin fasaha da zai ba da damar dawo da matatar cikin cikakken aiki.

Matatar ruwan, wadda gwamnatin Hungary ta gina tare da bai wa Najeriya a matsayin tallafin jin kai a shekarar 2023, tana da ƙarfin samar da kusan lita dubu 40 na tsaftataccen ruwa a kullum, wanda ke amfanar da kimanin mutane dubu 4.

Gwamnan ya bayyana cewa matatar ta daina aiki ne sakamakon matsalolin kula da ita da kuma gudanar da aikinta, inda ya ce gwamnatin jihar ta ɗauki matakin dawo da injiniyoyin da suka girka ta domin su taimaka wajen gano matsalar tare da magance ta.

Sanata Bala Mohammed ya gode wa gwamnatin Hungary da Kamfanin Hummels Water Engineering bisa haɗin gwiwa, yana mai jaddada aniyar gwamnatinsa na samar da ingantattun hanyoyin samun tsaftataccen ruwan sha ga al’ummar Jihar Bauchi.

Ya ce matakin na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na rage matsalar ƙarancin ruwan sha da inganta rayuwar al’ummomin da ke fama da ƙalubalen samun tsaftataccen ruwa.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sana'o'i, Sauran Duniya, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu Zai Shafe Makonni Uku A Hutun Shekara-Shekara
Next Post: Gwamna Inuwa Yahaya Ya Jaddada Haƙuri Da Fahimtar Juna A Siyasa

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Ya Taya Musulmai Murnar Sallah, Tare Da Kira Zuwa Ga Kishin Kasa Afrika
Kasashen Yankin Gulf Sun Bada Sanarwa Afrika
Hukumar ‘Yan Sanda Ta Dawo Da Dokar Zirga Zirgar Babura A Jihar Gombe Afrika
Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Biyan Hakkokin Tsofin Ma’aikata 800 Labarai
Iran Ta Kai Hari Matatar Mai A Kuwait Afrika
Aminu Tambuwal Ya Fice Daga PDP Ya Koma ADC Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sanda, Sojoji Da DSS Sun Ceto ‘Yan NYSC Da Aka Sace A Kogi
  • Rundunar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Al’umma Su Kiyaye Doka Yayin Bikin Takutaha
  • RUWASSA Ta Hada Masu Ruwa Da Tsaki Domin Inganta Aiwatar Da Shirin NG-SURWASH
  • Rundunar ’Yan Sandan Bauchi Ta Kama Dattijo Kan Zargin Cin Zarafin Yarinya ’Yar Shekara 8
  • Damara Ya Tallafa Wa Gasar Karatun Al-Qur’ani Da Naira Miliyan Biyar A Bambam

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • IBB: Ba Shakka Abiola Ya Lashe Zaben Yuni 12 Rediyo
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Zata Tabbatar Da Tsagaita Wuta A Kwango Afrika
  • Isra’ila Zata Karbi Mutanenta A Yankin Gaza Labarai
  • Babu Dabbar Da Zata Sake Shiga Amurka Daga Mexico! Amurka
  • NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya Najeriya
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Kara Sace Mutane A Jihar Naija! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Yi Ma Wasu Mutane Yankan Rago A Jihar Neja Labarai
  • Shugaba Tinubu Ya Ware Kudade Domin Bunkasa Rayuwar ‘Yan Najeriya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.