Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Amurka Da Najeriya Sunyi Hadakar Inganta Asibiticin Kiristoci
Published: December 22, 2025 at 2:12 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin Najeriya da ƙasar Amurka sun sanya hannu kan yarjejeniyar dala biliyan 5.1 don inganta asibitocin Kiristoci

Amurka da gwamnatin tarayyar Nijeriya sun kulla yarjejeniyar haɗin gwiwar kiwon lafiya ta tsawon shekaru biyar domin ƙarfafa tsarin kula da lafiya a Nijeriya.

Yarjejeniyar, wadda aka sanya hannu a ranar Asabar, ta tanadi kusan dala biliyan 2.1 daga Amurka, yayin da Nijeriya ta yi alƙawarin zuba kusan dala biliyan 3 daga cikin gida.

A cewar sanarwar da aka fitar, yarjejeniyar za ta mayar da hankali ne kan yaƙi da cututtuka kamar HIV/AIDS, tarin fuka, zazzabin cizon sauro, shan inna, da kuma rage mace-macen mata masu juna biyu da yara, waɗanda ke ci gaba da zama manyan ƙalubalen lafiyar jama’a a ƙasar.

Wani muhimmin ɓangare na yarjejeniyar shi ne tallafi na musamman ga cibiyoyin kiwon lafiya na addinin Kirista, waɗanda ke da kusan cibiyoyi 900 a faɗin Nijeriya.

Waɗannan cibiyoyin, da dama daga cikinsu suna aiki a yankunan karkara da wuraren da ke da ƙarancin ayyuka, suna ba da agaji ga sama da kashi 30 cikin 100 na al’ummar ƙasar.

Jami’an Amurka da na Nijeriya sun ce haɗin gwiwar za ta faɗaɗa damar samun ayyukan lafiya, ƙarfafa tsaron lafiya, da kuma gina tsarin kiwon lafiya mai ɗorewa sannan sun ƙara da cewa yarjejeniyar na nuna ƙudirin Nijeriya na ƙara kashe kuɗaɗe a fannin lafiya da kuma inganta sa ido kan cututtuka da martani ga ɓarkewar annoba.

Sai dai kuma, yarjejeniyar ta jawo ra’ayoyi mabanbanta daga jama’a, inda wasu ke yaba wa shigowar tallafin kuɗi, yayin da wasu ke nuna damuwa kan mai da hankali ga cibiyoyin addini a ƙasa mai tsarin mulki na zamani.

Amurka, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Kasashen AES Sun Buɗe Gidan Talabijin Na Bai Daya
Next Post: NDLEA Ta Fara Binciken Kwakwaf Akan Wasu ‘Yan Mata Dake Kai Kwaya Gidan Yari

Karin Labarai Masu Alaka

Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba Kiwon Lafiya
Shugabar Hamayya A Venezuela Ta Gana Da Paparoma Leo Amurka
An Bukaci Mabiya Addinin Kirista Da Suyi Koyi Da Rayuwar Yesu Najeriya
Sabon Magajin Garin New York Zai Soke Wasu Dokoki Amurka
Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi Najeriya
Wani Jirgi Yayi Saukar Angulu Ba Shiri Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kauran Bauchi: Muna Nan A PDP Daram! Siyasa
  • Gwamna Ahmad Aliyu Na Jihar Sokoto Ya Gabatar Da Kasafin Fiye Da Naira Biliyan 700 Labarai
  • Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar Afrika
  • Gwamnatin Kebbi Ta Samu Tankokin Yaki Tsaro
  • Anyi Rashin ‘Yan Jarida 6 A Jihar Gombe Sakamakon Hatsarin Mota Labarai
  • Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Masu Garkuwar da Mutane a Jihar Gombe Tsaro
  • NUJ: Akwai Bukatar Samar Da Inshorar Lafiya Ga ‘Yan Jarida A Najeriya Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.