Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Najeriya Ta Taya Super Eagles Murnar Lashe Tagulla A Gasar AFCON
Published: January 18, 2026 at 10:12 AM | By: Bala Hassan | Updated: January 18, 2026

Gwamnatin Tarayya ta taya Super Eagles murna bisa samun lambar tagulla a gasar AFCON.

Gwamnatin Tarayya ta taya ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Super Eagles murna bisa samun lambar yabo ta tagulla a gasar Kofin Nahiyar Afrika (AFCON) ta 2025, inda ta bayyana rawar da ƙungiyar ta taka a matsayin abin alfahari da farin ciki ga ’yan Nijeriya.

A cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Asabar, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jinjina wa ‘yan ƙungiyar bisa yadda suka ɗaukaka tarihin ƙwallon ƙafa na Nijeriya da zuciya ɗaya, ƙwarewa, da jajircewa a tsawon gasar.

A cewar Ministan, Super Eagles sun nuna jarumta, haɗin kai, da amincewa da juna tun daga matakin rukunoni har zuwa busar ƙarshe a birnin Kasablanca na ƙasar Marokko, wanda hakan ya zaburar da miliyoyin ‘yan Nijeriya a gida da kuma ƙasashen waje.

Ya bayyana cewa irin wasan da suka yi ya wuce kawai buga ƙwallo, domin ya farfaɗo da kishin ƙasa da kuma kyakkyawar fata.

Ministan ya ce samun lambar tagulla ya sake ƙara wa tarihin nasarorin Nijeriya armashi a gasar AFCON, tare da ƙarfafa martabar da Super Eagles ke da ita a nahiyar.

Ya yaba wa ladabi da ruhin gwagwarmaya na ƙungiyar, musamman a wasannin da suka fafata da gaggan ƙungiyoyi.

Haka kuma, ya miƙa godiyar sa ga masu horaswa, ma’aikatan tallafi, da ‘yan wasan bisa sadaukarwa da jajircewar su duk da ƙalubalen da suka fuskanta.

Ya jaddada cewa wasan nasu ya nuna muhimmancin aiki tare, imani, da alfahari wajen wakiltar Nijeriya, ya ƙara da cewa wannan ƙoƙari ya sake tabbatar da matsayin Nijeriya a matsayin babbar ƙasa a ƙwallon ƙafar Afrika.

Ko da yake ya bayyana cewa babban kofin ta suɓuce musu a wannan karo, Ministan ya jaddada cewa an samu lambar tagullar cikin mutunci da ƙoƙari, kuma ba ta ‘yan wasan ba ce kawai, har ma ta ɗaukacin ‘yan Nijeriya ce waɗanda suka ba su goyon baya kuma suka yi imani da su a duk tsawon gasar.

Ya buƙaci Super Eagles da su yi murnar wannan nasara cikin alfahari, tare da ɗaukar ta a matsayin abin ƙarfafa gwiwa domin tunkarar duk wani ƙalubale nan gaba, sannan ya nuna godiya da jinjina kan yadda suka wakilci ƙasar nan.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: FRSC Gombe: Hatsarin Mota Ya Yayi Ajalin Mutane 38 Ya Jikkata Fiye Da 218 A Wata Ɗaya
Next Post: ADC Ta Sha Damarar Gwabzawa Da APC A Zaben 2027

Karin Labarai Masu Alaka

Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz Wasanni
An Shirya Taron Horas Da Matasa Gabanin Wasan Motsa Jiki 2025 Wasanni
An Bude Gasar Kwallon Kafa Ta Mata A Najeriya NWFL 2025 Wasanni
Barcelona Ta Lashe Kofin Spanish Super Cup  Wasanni
CAF Ta Ci Tarar Ƙasar Masar Dala 5,000 AFCON 2025 Wasanni
Messi Da Cristiano Suna Da Tasiri A Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Salmanu: Ci Gaban Wikki Tourist FC Shine A Gaba Na Wasanni
  • Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane Tsaro
  • Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Gombe Ya Ziyarci Pindiga Labarai
  • Jakadan Amurka A Poland Ya Yanke Hulda Da Kakakin Majalisar Kasar Labarai
  • Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Kasafin Kudi Mai Sauya Fasali Da Karfafa Rayuwar Al’umma Labarai
  • Kimanin Ganga Miliyan 40 Na Danyen Albarkatun Mai Yayi Kwantai A Kasashen Afirka Ta Yamma Afrika
  • Shugaban Amurka Donald Trump Ya Nanata Aniyar Mallakar Greeland Daga Kasar Denmark Amurka
  • Amurka Ta Bada Tabbacin Baiwa Ukraine Tsaron Na Shekaru 15 Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.