Gwamnatin Tarayya ta taya Super Eagles murna bisa samun lambar tagulla a gasar AFCON.
Gwamnatin Tarayya ta taya ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Super Eagles murna bisa samun lambar yabo ta tagulla a gasar Kofin Nahiyar Afrika (AFCON) ta 2025, inda ta bayyana rawar da ƙungiyar ta taka a matsayin abin alfahari da farin ciki ga ’yan Nijeriya.
A cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Asabar, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jinjina wa ‘yan ƙungiyar bisa yadda suka ɗaukaka tarihin ƙwallon ƙafa na Nijeriya da zuciya ɗaya, ƙwarewa, da jajircewa a tsawon gasar.
A cewar Ministan, Super Eagles sun nuna jarumta, haɗin kai, da amincewa da juna tun daga matakin rukunoni har zuwa busar ƙarshe a birnin Kasablanca na ƙasar Marokko, wanda hakan ya zaburar da miliyoyin ‘yan Nijeriya a gida da kuma ƙasashen waje.
Ya bayyana cewa irin wasan da suka yi ya wuce kawai buga ƙwallo, domin ya farfaɗo da kishin ƙasa da kuma kyakkyawar fata.
Ministan ya ce samun lambar tagulla ya sake ƙara wa tarihin nasarorin Nijeriya armashi a gasar AFCON, tare da ƙarfafa martabar da Super Eagles ke da ita a nahiyar.
Ya yaba wa ladabi da ruhin gwagwarmaya na ƙungiyar, musamman a wasannin da suka fafata da gaggan ƙungiyoyi.
Haka kuma, ya miƙa godiyar sa ga masu horaswa, ma’aikatan tallafi, da ‘yan wasan bisa sadaukarwa da jajircewar su duk da ƙalubalen da suka fuskanta.
Ya jaddada cewa wasan nasu ya nuna muhimmancin aiki tare, imani, da alfahari wajen wakiltar Nijeriya, ya ƙara da cewa wannan ƙoƙari ya sake tabbatar da matsayin Nijeriya a matsayin babbar ƙasa a ƙwallon ƙafar Afrika.
Ko da yake ya bayyana cewa babban kofin ta suɓuce musu a wannan karo, Ministan ya jaddada cewa an samu lambar tagullar cikin mutunci da ƙoƙari, kuma ba ta ‘yan wasan ba ce kawai, har ma ta ɗaukacin ‘yan Nijeriya ce waɗanda suka ba su goyon baya kuma suka yi imani da su a duk tsawon gasar.
Ya buƙaci Super Eagles da su yi murnar wannan nasara cikin alfahari, tare da ɗaukar ta a matsayin abin ƙarfafa gwiwa domin tunkarar duk wani ƙalubale nan gaba, sannan ya nuna godiya da jinjina kan yadda suka wakilci ƙasar nan.


