Ma’aikatar albarkatun ma’adinai ta musanta zargin da kungiyar dattan Arewa (NEF) ta yi cewa gwamnatin tarayya ta kafa masana’antar sarrafa gwal a Legas tare da karya ƙa’idar daidaiton tarayya.
A wata sanarwa da Segun Tomori, mataimaki na musamman kan yaɗa labarai ga ministan albarkatun ma’adinai, Dele Alake, ya fitar, ya bayyana cewa masana’antar da ake magana a kai ba ta gwamnati ba ce, illa dai aikin kamfanin Kian Smith mai zaman kansa.
Tomori ya ce babu inda ministan ya taɓa bayyana cewa gwamnati ce ta mallaki ko ta kafa masana’antar gwal a Legas, yana mai ƙara da cewa dukkan masana’antun gwal da ake shirin ƙaddamarwa a sassan ƙasar mallakar kamfanoni masu zaman kansu ne.
Ya bayyana cewa masana’antar ta zo ne sakamakon manufar ƙara darajar albarkatu da ma’aikatar ta ƙaddamar shekaru biyu da suka gabata, wadda ke ƙarfafa sarrafa ma’adinai a cikin gida maimakon fitar da su danye.
Tomori ya kuma soki NEF bisa abin da ya kira rashin yin bincike kafin fitar da zargi, yana mai cewa ba zai yiwu a tilasta wa kamfani mai zaman kansa ya kafa aikinsa a wani yanki na musamman ba.
A ƙarshe, ya buƙaci NEF da ta goyi bayan ƙoƙarin Shugaba Bola Tinubu na bunƙasa tattalin arzikin ƙasa da ƙarfafa dogaro da kai.


