Ranar Alhamis gwamnatin shugaba Donald Trump ta kakabawa Iran wasu sabbin takunkumi, wadda ta auna kan sifiri ta ruwa, kamfanoni da suke kasuwanci ta fuskar makamashi, kamar yadda bayanai a shafin internet na hukumar baitul malin Amurka suka nuna .
Wadannan sabbin takunkumin suna zuwa ne a dai dai lokacin da hukumomi a Farisa ko Iran suke daukar matakai masu tsanani na murkushe masu zanga zanga a duk fadin kasar wadda aka fara tun ranar 28 ga watan jiya.
Haka nan takunkumin zai shafi wasu daidaikun mutane su 11, da kuma gidan yarin Iran da ake kira Fardis.


