Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Hukumar NAPTIP Ta Kubutar Da Yara 11 Daga Hannun Masu Safara Mutane
Published: December 15, 2025 at 2:16 PM | By: Mahmud Kwari | Updated: December 16, 2025

Hukumar NAPTIP, dake yaki da safara da fataucin bil’adama a Najeriya, ta dakile yunkurin wasu bata gari na safarar wasu yara su 11 ‘yan asalin jihar Jigawa a yankin arewa maso yammacin Najeriya. Hukumar tace tuni ta mika yaran da Jami’an ta suka kubutar ga majalisar karamar hukumar Ringim ta jihar Jigawa.

Kwamandan hukumar a jihar ta Jigawa Abdulkadir Turajo ya fada yayin taron masu ruwa da tsaki a Dutse, shalkwatar jihar cewa, jami’an hukumar ta NAPTIP sunyi nasarar kubutar da yaran a birnin Lokoja na jihar Kogi yayin da ake kokarin kai su wani wurin da ba’a bayyana ba.

Yace yaran wadanda dukkanin su maza ne zalla, ‘yan shekaru 7 zuwa 15, an kwaso su ne daga kauyukan Tsaba da Kunkurawa da kuma Tsabare a karamar hukumar Ringim ta jihar ta Jigawa.

Kwamandan hukumar ta NAPTIP a Jigawa ya yabawa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar da kuma hadin kan da suka baiwa hukumar wajen sada yaran da iyayen su cikin hanzari.

Batun safarar yara kanana, galibi daga yankin arewaci zuwa kudancin Najeriya wani kalubale da hukumomin kasar ba su kai ga magance shi ba, duk da cewa, iyaye yara a yankin na arewacin Najeriya sun dade suna kokawa dangane da wannan matsala.

A shekarun baya baya nan, wannan matsala tayi kamari a Jihar Kano, jiha mafi yawan Jama’a a kasar, al’amarin daya kai ga hukumomin jihar sun kafa wani kwamitin bincike mai karfi domin lalubo hanyoyin dakile wannan matsala da galibi aka gano cewa, ana boye yaran ne jihohin Enugu da Abia bayan an yi safarar su daga Kano.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Hukumar Hisbah Ta Kona Barasar Dubban Nairori A Katsina
Next Post: Rikici Ya Barke A Kano Bayan Kashe Wani Matashi Da Ake Zargi Da Kashe Ladani

Karin Labarai Masu Alaka

Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa Labarai
Menene Illar Yada Labaran Karya A Kafofin Sada Zumunta Na Zamani Labarai
Shugaba Tinubu Ya Nada Shugaban NAHCON Labarai
Shugaban Kasar Uganda Yana Kokarin Mayar Da Mulkin Kasar Na Gado Labarai
Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Matsalar Tsaro A Shiyar Labarai
Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi Najeriya
  • Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin Kuɗin 2026 Najeriya
  • Fadar Sarkin Musulmi: Talata Ne 1 Ga Watan Sha’aban Na 1447AH Najeriya
  • Yan Fashi Sun Shiga Gidan Alex Iwobi A Ingila Wasanni
  • Jam’iyar NNPP: Abba Kabir Yusuf Yaci Amanar Mu Siyasa
  • Iran Tabada Tabbacin Cigaba Da Rufe Mashigar Hormuz Afrika
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Afrika
  • Mutane Kusan 30 Ne Suka Mutu a Nguru Dake Jihar Yobe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.