Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Hukumar NAPTIP Ta Kubutar Da Yara 11 Daga Hannun Masu Safara Mutane
Published: December 15, 2025 at 2:16 PM | By: Mahmud Kwari | Updated: December 16, 2025

Hukumar NAPTIP, dake yaki da safara da fataucin bil’adama a Najeriya, ta dakile yunkurin wasu bata gari na safarar wasu yara su 11 ‘yan asalin jihar Jigawa a yankin arewa maso yammacin Najeriya. Hukumar tace tuni ta mika yaran da Jami’an ta suka kubutar ga majalisar karamar hukumar Ringim ta jihar Jigawa.

Kwamandan hukumar a jihar ta Jigawa Abdulkadir Turajo ya fada yayin taron masu ruwa da tsaki a Dutse, shalkwatar jihar cewa, jami’an hukumar ta NAPTIP sunyi nasarar kubutar da yaran a birnin Lokoja na jihar Kogi yayin da ake kokarin kai su wani wurin da ba’a bayyana ba.

Yace yaran wadanda dukkanin su maza ne zalla, ‘yan shekaru 7 zuwa 15, an kwaso su ne daga kauyukan Tsaba da Kunkurawa da kuma Tsabare a karamar hukumar Ringim ta jihar ta Jigawa.

Kwamandan hukumar ta NAPTIP a Jigawa ya yabawa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar da kuma hadin kan da suka baiwa hukumar wajen sada yaran da iyayen su cikin hanzari.

Batun safarar yara kanana, galibi daga yankin arewaci zuwa kudancin Najeriya wani kalubale da hukumomin kasar ba su kai ga magance shi ba, duk da cewa, iyaye yara a yankin na arewacin Najeriya sun dade suna kokawa dangane da wannan matsala.

A shekarun baya baya nan, wannan matsala tayi kamari a Jihar Kano, jiha mafi yawan Jama’a a kasar, al’amarin daya kai ga hukumomin jihar sun kafa wani kwamitin bincike mai karfi domin lalubo hanyoyin dakile wannan matsala da galibi aka gano cewa, ana boye yaran ne jihohin Enugu da Abia bayan an yi safarar su daga Kano.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Hukumar Hisbah Ta Kona Barasar Dubban Nairori A Katsina
Next Post: Rikici Ya Barke A Kano Bayan Kashe Wani Matashi Da Ake Zargi Da Kashe Ladani

Karin Labarai Masu Alaka

Rikici Tsakanin NNPC Da Kungiyar Gwamnoni Akan Gibin Kudade Labarai
Majalisar Tarayya Ta Amince Da Mutane Uku A Matsayin Jakadun Kasashen Waje Labarai
Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026 Labarai
An Gano Wani Kurkukun Sirri Da Ake Azaftar Da Mutane A Kasar Libya Afrika
‘Yan Tada Kayar Baya Sun Tayar Da Bom A Maiduguri Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet
  • Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado
  • Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia
  • Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Eziekel Gomos Ya Zamo Babban Daraktan Sakatariyar Zauren Gwamnonin Arewa Najeriya
  • Shugaban Kasar Amurka Yakara Hana Wasu Kasashe Shiga Amurka Ciki Harda Nijar Amurka
  • Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
  • Kasashen Daular Larabawa Tare Da Saudiya Da Jordan Sunyi Allah Wadai Da kasar Israel Afrika
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai
  • Wata Tankar Mai Ta Kife A Apapa Legas Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mayakan ISWAP Sun Kai Farmaki Kan Sojojin Najeriya Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.