Hukumar NAPTIP, dake yaki da safara da fataucin bil’adama a Najeriya, ta dakile yunkurin wasu bata gari na safarar wasu yara su 11 ‘yan asalin jihar Jigawa a yankin arewa maso yammacin Najeriya. Hukumar tace tuni ta mika yaran da Jami’an ta suka kubutar ga majalisar karamar hukumar Ringim ta jihar Jigawa.
Kwamandan hukumar a jihar ta Jigawa Abdulkadir Turajo ya fada yayin taron masu ruwa da tsaki a Dutse, shalkwatar jihar cewa, jami’an hukumar ta NAPTIP sunyi nasarar kubutar da yaran a birnin Lokoja na jihar Kogi yayin da ake kokarin kai su wani wurin da ba’a bayyana ba.
Yace yaran wadanda dukkanin su maza ne zalla, ‘yan shekaru 7 zuwa 15, an kwaso su ne daga kauyukan Tsaba da Kunkurawa da kuma Tsabare a karamar hukumar Ringim ta jihar ta Jigawa.
Kwamandan hukumar ta NAPTIP a Jigawa ya yabawa ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar da kuma hadin kan da suka baiwa hukumar wajen sada yaran da iyayen su cikin hanzari.
Batun safarar yara kanana, galibi daga yankin arewaci zuwa kudancin Najeriya wani kalubale da hukumomin kasar ba su kai ga magance shi ba, duk da cewa, iyaye yara a yankin na arewacin Najeriya sun dade suna kokawa dangane da wannan matsala.
A shekarun baya baya nan, wannan matsala tayi kamari a Jihar Kano, jiha mafi yawan Jama’a a kasar, al’amarin daya kai ga hukumomin jihar sun kafa wani kwamitin bincike mai karfi domin lalubo hanyoyin dakile wannan matsala da galibi aka gano cewa, ana boye yaran ne jihohin Enugu da Abia bayan an yi safarar su daga Kano.


