Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Limamin Da Ya Ceci Kiristoci Lokacin Rikicin Addini A Jihar Filato Ya Rasu
Published: January 16, 2026 at 12:16 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 16, 2026

Limamin addinin Islama daya ya sami shahara har ya sami lambobin yabo kan zaman lafiya a jahar Filato, Imam Abdullahi Abubakar ya rasu a Jos.

Marigayi Imam Abdullahi Abubakar ya shahara a duniya ne biyo bayan sadaukar da kai da yayi na bada kariya ga mabiya addinin Kirista fiye da dari uku, bayan ‘yan bindiga sun kai musu hari a kauyen Yalwan Gindin Akwati dake karamar hukumar Barkin Ladi a shekarun baya.

A ranar Alhamis goma sha biyar ga watan Janairun dubu biyu da ishirin ta shida, da misalin karfe tara na dare ne, Allah ya karbi ran Imam Abdullahi Abubakar bayan fama da rashin lafiya.

Malamin, wanda yayi limanci a karkara, musamman a yankin da a baya ake samun yawan tashin hankali, ya taimaka kwarai wajen wanzadda zaman lafiya da hadin kai tsakanin mabiya addinai da kabilu daban-daban, wanda ya kai ga har kasashen duniya irin su Amurka da Saudi Arebiya da kungiyoyi masu zaman kansu da gwamnatocin tarayya da na jahar Filato suka bashi lambobin yabo da adadinsu ya kai goma sha hudu.

A zantawarsa da wakiliyar GTA Hausa a Jos, Zainab Babaji, kafin rasuwarsa, Imam Abdullahi Abubakar ya bayyana cewa yana sauke hakkinsa na zama da kowa lafiya ne, kamar yadda Allah ya hori al’umma suyi, don haka ya sadaukar da ransa wajen ceton Kirista fiye da dari uku, a lokacin da ‘yan bindiga suka mamayesu.

Imam yace a dalilin ayyukan zaman lafiya da yayi, ya sami lambobin yabo, ya kuma je aikin Hajji banda ganawa da yayi da manyan shugabannin duniya ciki har da marigayi, shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari da wassu gwamnoni.

Malam Abdullahi Umar Hassan, na’ibin limamin masallacin da Imam Abdullahi Abubakar ya jagoranta, ya bayyana mamacin a matsayin mai son hada kan jama’a ba tare da nuna bambanci ba.

Malam Hassan yayi fatar Allah ya zabo wanda zai cike gurbin da Imam ya bari na wanzadda zaman lafiya.

Haka ma kafafen sada zumunta a yau Jumma’a sun cika da hotunan Imam Abdullahi Abubakar, musammman daga wadanda suka yi hulda dashi a lokacin da yake raye, suna bayyana alhininsu kan rashin dattijon, da zayyana irin ayyukan alkhairi da yayi na samadda zaman lafiya.

Ga Rahoton Zainab Babaji Daga Jos

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/AUD-20260116-WA0025.mp3
Labarai

Post navigation

Previous Post: Dan Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya Atiku Abubakar Ya Shiga Jam’iyyar APC
Next Post: Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane

Karin Labarai Masu Alaka

Ministan Sadarwan Kasar Uganda Yayi Allah Wadai Da Kaiwa Bobi Wine Hari Afrika
Sojin Kasar Congo Da ‘Yan Tawaye Sun Kara Shiga Yankin Uvira Labarai
Kasashen Turai: Bazamu Yarda Da Dokar Harajin Trump Ba Labarai
Iran Tace Farisa Zata Kai Hari Kan Mayakan Amurka Amurka
Wasu Muhimman Abubuwa Da Najeriya Ba Zata Manta Da Su Ba A 2025 Labarai
Kama Muhyi Magaji Siyasa ce Kawai Inji Gwamnatin Kano Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya Amurka
  • Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai Amurka
  • Anfara Tantance Lafiyar Maniyyatan Jihar Gombe Kiwon Lafiya
  • An Dakatar Da Daniel Bisa Zargin Fyade Wasanni
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031 Wasanni
  • Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara Labarai
  • Dangote Ya Rage Farashin Mai A Najeriya Labarai
  • Birtaniya Ta Bukaci Israela Ta Janye Shawarar Fadada Iko Da Kogin Jordan Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.