Isra’ila ta kashe ministan leƙen asirin Iran yayin da take ci gaba da yaƙin neman kai hari kan manyan shugabannin Jamhuriyar Musulunci, kuma an ruwaito cewa ta kai hari kan wata tashar iskar gas ta teku mallakar Iran a jiya Laraba, yayin da yaƙin ke ƙara matsa lamba kan tushen tattalin arzikin makamashi.
Iran ta yi Allah-wadai da harin da aka kai kan babbar cibiyar iskar gas ta South Pars, inda Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya yi gargadin “sakamakon da ba za a iya shawo kansa ba” wanda “zai iya shafar duk duniya.”
Iran ta ci gaba da kai hare-hare kan cibiyoyin makamashi na maƙwabtan ta a yankin Tekun Fasha, inda ta kai hari kan wata babbar cibiyar iskar gas a Qatar, yayin da kuma take ci gaba da matsa lamba kan mashigin ruwa na Hormuz wanda kusan kashi ɗaya cikin biyar na man fetur na duniya ke bi ta cikinsa.
Farashin mai ya sake tashi da wani ƙarin kashi 5%, ya haura dala $108 kowace ganga a kasuwannin duniya, wanda hakan ke ƙara tsadar man fetur da sauran kayayyaki.
Farashin danyen mai na Brent, wanda ake amfani da shi a matsayin ma’aunin duniya, yanzu ya kusan tashi da kashi 50% tun bayan fara yaƙin.


