Jami’ai a Afirka suna gargadin cewa tashin goron zabbi da farashin mai yayi sakamakon yakin Iran, zaiyi kalubale ga manufofin tattalin arziki, kuma zaiyi illa ga a wasu muhiman sassa kamar hakar ma’adinai, wadda hakkan zai dagula farfadowar tattalin arzikin kasashe da suke nahiyar.
Manyan bankuna a birane daga Accra zuwa Luanda suna ta rage kudin ruwa a cikin watannin baya bayan nan ganin yadda ake samun faduwar farashin kayayyaki, da kuma samun daidaito a fannin canjin kudaden ketare, da nufin zaburadda tattalin arzikin su. Da alamun yanzu wadannan matakan za su tsaya.
Babban bankin Uganda ne kadai a nahiyar tun ma gabannin fara yakin ya fara taka-tsan-tsan, yanzu yace zai sake nazarin tasirin manufofin ganin sabon kalubalen.
A ranar Alhamis, babban bankin Angola bai rage ko ya kara kudin ruwan da bankuna suke caji a kasar ba, har aka ji gwamnan babban bankin Manuel Tiago Dias yana cewa, kasadar da tattalin arzikin Kasashen ke fuskanta shine tsawon lokaci da yakin zai dauka, wadda zai shafi jigilar taki da sauran su.
Haka nan ana sa ran cewa wasu manyan bankunan kasashe da suke yankin kama daga Ghana, da Najeriya, da Zambia, da ma Kenya duk za su dakatar da matakan sassauta kudin ruwa da bankunan suke karba.


