kamfanin man fetur na Nigeria NNPC, na tattaunawa da wani kamfani a kasar China kan daya daga cikin matatun man fetur na kasa, a cewar shugaban NNPC a ranar Laraba.
Shugaban kamfanin NNPC, Bayo Ojulari, yace kamfanin na neman kwararru a matsayin abokan kasuwanci na hannun jari don su farfado da matatun man kamfanin 4, bayan da aka shafe shekaru ana tafka asara don rashin aiki yadda ya kamata.
Ya ce wani bincike da aka gudanar, kwanaki kadan bayan ya kama matsayin aiki a watan Aprilun bara, ya nuna cewa ana tafka asara a matatun man, tare da kashe kudaden aiki masu yawa, da kuma biyan ‘yan kwangila makudan kudade, yayin da adadin abin da ake samu daga matatun ya ci gaba da yin kasa.


