Rawar da China take takawa a zaman wacce take kan gaba wajen bada bashi ga kasashe masu tasowa, ya sauya cikin shekaru 10 da suka wuce, yayin da sabbin basussuka ga kasashe matalauta yake faduwa, yawan kudade da kasashen suke biyan China sun karu sosai, kamar yadda alkaluma daga wata cibiya da ake kira ONE DATA suka nuna.
Chanjin yana zuwa ne a dai dai lokacin da basussuka da kasashe matalauta suke karba daga kungiyoyi da hukumomin kasa da kasa suka karu, da kamar kashi 124 cikin shekaru 10 da suka wuce, wanda yanzu sune ke bada kashi 56 cikin dari na basussuka da kasashen suke karpa daga ketare, da suka kai kimnin dala bilyan 379 da aka bayar tsakanin shekara ta 2020-2024, kididdigar ta nuna.
A bayanai da ake da su na baya bayan nan, daga shekara ta 2020-2024, Afirka taga tasirin mafi girma inda kudade dala bilyan 30 suka shiga baitul mali wasu kasashe dake nahiyar tsakanin shekara 2015-2019, yayin da bilyan 22 ya fita a zaman biyan bashi.
A halin da ake ciki kuma, an fara shari’ar tsohuwar ministan mai ta Najeriya Allison Madueke, ranar Talata, inda masu gabatar da kara suka ce ta karbi cin hanci da rashawa domin bada ayyukan kwangila ta fuskar Makamashi.
A gefe daya kuma, gwamnatin jihar Nija a Najeriya zata yi aiki da Bankin Islama domin habaka samarda makamashi ta rana, kan kudi dala milyan 163, domin kara samarda wutan lantarki da zai taimakawa ayyukan noma da masana’antu, kamar yadda jami’ai suka fada ranar talata.


