Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kasar Togo Ta Kori Paul Henri Damiba Zuwa Kasar Sa Ta Haihuwa
Published: January 21, 2026 at 5:38 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hukumomi a kasar Togo sun kame tare da korar tsohon shugaban kasar Burkina Faso, Paul Henri Damiba, zuwa kasar sa ta haihuwa, bayan da gwamnati ta zarge shi da laifin yunkurin juyin mulki, kamar yadda wasu majiyoyi 2 suka shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters ranar Talata.

Paul Henri Damiba, ya karbi ragamar mulki ne a shekarar 2022, bayan da aka yiwa gwamnatin farar hula ta Burkina faso juyin mulki, wadda farin jinin ta ya dusashe saboda yawan tashin hankali da ake samu daga ‘yan ta’adda.

Rashin nasarar Damiba wajen dakile hare-haren ‘yan ta’adda, ya haifar da fushin sojin kasar, abinda ya jawo shima aka tsige shi a wannan shekarar, a wani juyin mulki karkashin Ibrahim Traore, wanda a yanzu shi ne shugaban kasar karkashin mulkin soja.

A farkon Wannan watan ne Burkina Faso ta sanar cewa ta dakile wani yunkuri na kashe shugaba Traore, da ake zargin Damiba ne ya shirya, wanda ya nemi mafaka a Lome, babban birnin kasar Togo.

Wani jami’in tsaro da wani dake da kusanci da shugaban kasar Togo sun shaidawa kamfanin dillacin labarai na Reuters ranar Talata cewa An kama Damiba ranar Asabar, kuma An dauke shi a jirgi zuwa Ouagadougou, babban birnin Burkina Faso.

Togo ta tabbatar da fitar da Damiba daga kasar, inda ta ce ta yi haka ne, bisa bukata daga Burkina Faso.

Laifukan da ake tuhumar Damiba a Burkina Faso da su sun hada da almubazzaranci da wadaka da kudaden al’umma da halarta kudin haram, a cewar gwamnatin Togo

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Sojin Najeriya Da ‘Yan Ta’adda Sunyi Taho Mugama
Next Post: Turkiyya Tana Gudanar Da Binciken Kasar Da Suka Kona Tutar Ta

Karin Labarai Masu Alaka

Samar Da Albarkatun Mai Ya Ragu A Iraq Afrika
Hamas Ta Kwance Damara Afrika
Jirgin Sama Ya Fadi A Kano Labarai
Shugaban Kasar Najeriya Ya Nada Sabon Ministan Kudi Labarai
Gwamnatin Amurka Na Kokarin Watsi Da Tsohuwar Dokar Jones Labarai
Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ministan Harkokin Wajen Rasha Dana Iran Sun Tattauna Don Kawo Karshen Yaki A Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Hukumar Ƴan Sanda Ta Musanta Zargin Kashe Ɗan Achaba a Gombe Tsaro
  • Kasar Netherland Ta Mayarwa Masar Mutum Mutumin Tarihi Afrika
  • Gwamnatin Gombe Ta Raba Naira Miliyan 14 Ga Iyalen ‘Yan Jaridan Da Suka Rasu Najeriya
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane Takwas Da Ake Zargi Da Siyar Da Tikitin AFCON Ba Bisa Ka’ida Ba Wasanni
  • Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.