Shugaban ƙasar Faransa Emmanuel Macron ya bayyana barazanar harajin da takwaransa na Amurka Donald Trump ya yi a matsayin abin da ba za su amince da shi ba, yana mai cewa babu barazanar da za ta tursasa ƙasashen Turai su yi abin da ba haka ba.
Shugaban na Faransa ya ci gaba da cewa, muddin Trump ya aiwatar da harajin da yake iƙirari, shakka babu za su mayar da martani, kuma cikin haɗin kai.
Wannan kalamai na Macron na zuwa ne, daidai lokacin da Firaministan Sweden, Ulf Kristersson ke bayyana cewa, babu wata ƙasa da ta isa ta tursasa su yin abin da basu yi niyya ba.
Yanzu haka dai ƙasar Jamus ta ce tana nazartar kalaman Mista Trump, kuma tuni ta fara tuntuɓar takwarorinta na Turai domin jin ina aka kwana a ragaya.
Kusan za a iya cewa dai kasashen Turai da alama matsayarsu ɗaya ce, domin itama Birtaniya ta bakin jagorar jam’iyyar Conservative, Kemi Badenoch ta ce sun karkata kan matsayar Firaministan ƙasar, tare da cewa suna goyon bayan al’ummar Birtaniya game da makomar yankin na Greenland.


