Kamfanin dillancin labaran Koriya ta Arewa, ya ba da rahoton cewa ranar lahadi, kasar ta gudanar da gwajin harba makamai masu linzami masu tsananin gudu, a wani matakin auna irin karfin sojojinta da makamansu na kare kai.
Shugaba Kim Jong Un, wanda ya sanya idanu wajen harba makaman, yace mataki ne mai matukar muhimmanci ga kasar ta ci gaba da kasancewa tana da karfin makaman nukiliya, ko ta fadada su, domin zamowa hannunka mai sanda ga duk mai neman kai mata farmaki.
Kamfanin dillancin labaran na KCNA yace makaman sun fada kan inda aka auna su kimanin kilomita dubu daya a tekun dake gabas da Koriya ta Arewa.
A ranar lahadi, rundunar sojojin Koriya ta Kudu, ta ce Arewa ta harba makamai masu linzami a tekun dake gabas da kasar a daidai lokacin da shugaban Koriya ta Kudu, Lee Jae Myung ya fara ziyarar aiki a kasar China.
Harba wadannan makamai masu linzami masu tsananin gudu da Koriya ta Arewa ta yi, ya biyo bayan fitowar da ta yi tana yin Allah wadarai da harin da Amurka ta kai a kan Venezuela a zaman wanda ya keta haddin diyaucin kasar.



