Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kungiyar ECOWAS Ta Koka Game Da Yawan Juyin Mulki A Kasashen Afirka
Published: December 15, 2025 at 6:23 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Afirka ta Yamma, ECOWAS ko CDEAO, ta bayyana rashi yardarta da shirin mayar da mulki hannun farar hula da shugabannin mulkin soja na Guinea-Bissau, suka bayyana, tana mai bukatar da a gaggauta maido da aiki da tsarin mulki.

Shugabannin ECOWAS, sun yi barazanar saka takunkumi na musamman a kan duk wadanda ke kawo cikas ga maido da mulkin farar hula a kasar.

A ranar 26 ga watan Nuwamba ne wasu hafsoshin soja a Guinea-Bissau suka hambarar da shugaba Umaro Sissoco Embalo, kwana daya kafin a bayyana sakamakon zaben shugaban kasa, kashegari kuma suka ayyana Manjo Janar Horta Inta-a a matsayin shugaban gwamnatin mulkin soja na wuin gadi.

Wannan juyin mulki da aka yi a Gyuinea-Bissau, shine na tara cikin shekaru 5 da suka shige a yankin yammaci da tsakiyar Afirka, abinda ya kara irin fargabar da ake yi ta zaizayewar mulkin dimokuradiyya a wannan yanki mai fama da rashin tsaro da rashin kwanciyar hankalin siyasa.

Shugabannin dake halartar taron kolin shekara na kungiyar ECOWAS ranar lahadi a Abuja, babban birnin Najeriya, sun yi kiran da a sako dukkan ‘yan siyasar da aka kama, ciki har da shugabannin hamayya, a kuma tsara shirin maida mulki cikin gaggawa wanda zai kumshi dukkan sassan kasar cikin gaggawa.

Shugaban majalisar zartasa ta kungiyar ECOWAS, Omar Touray, yace matakin da shugabannin kungiyar suka dauka shine na tabbatar da cewa sam ba za a taba yarda da sauya gwamnati ta hanyar da tsarin mulki bai amince ba.

ECOWAS ta ce ‘yan kallonta, da na Kungiyar Tarayyar Afirka da na kasashe masu magana da harshen Portugal duk sun ce zaben shugaban kasa da aka gudanar a Guinea-Bissau, an yi shi cikin adalci.

Har ila yau kungiyar ta umurci shugabanta da ya jagoranci wata tawaga ta manyan jami’ai zuwa Gyuinea-Bissau domin tattaunawa da hukumomin sojan kasar.

Afrika

Post navigation

Previous Post: An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi
Next Post: ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya

Karin Labarai Masu Alaka

An Gudanar Da Zanga-Zanga A Guinea-Bissau Afrika
Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma Afrika
Sojojin Da Suka Kifar Da Farar Hula A Guinea-Bissau Sun Sanar Da Cewa! Afrika
An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan Afrika
Sanyin Hunturu Yayi Ajalin ‘Yan Cirani A Morocco Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya
  • Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati
  • Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno
  • A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela
  • Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Arteta, Arsenal Zata Yi Sauye-Sauye A Janairu, Wasanni
  • Gwannatin Jihar Kebbi Ta Arawa Maniyyata Kuɗin Aikin Hajji 2026, Labarai
  • Kyautata Dangantaka Tsakanin Jami’an Tsaro Da Al’umma Ce Mafita Najeriya
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Talata 11.18.2025 Rediyo
  • Alkalan Wasannin Kwallon Kafa A Ghana Zasu Samu Inshora Wasanni
  • Umar Aliyu, Shugaban Magoya Bayan Wikki Tourist
    Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo Wasanni
  • Gangamin Wayar Da Kai Don Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Jihar Gombe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.