Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kungiyar Enyimba: Bamu Da Niyyar Rage Albashin ‘Yan-Wasa
Published: November 20, 2025 at 3:25 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 20, 2025

Kungiyar Kwallon Kafa ta Enyimba dake ABA a Najeriya ta fidda wata takarda wacce ta raba wa manema labarai. Takardar dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na ƙungiyar SAMPSON ORJI.

Inda suke nisanta kansu da wani labari da ya ja hankali a shafin sada zumuntar zamani cewar ƙungiyar ta Enyimba FC. Ta rage Albashin ‘Yan Wasa da kashi 50% bayan shan kaye a gida a hannun Wikki Tourist FC. daci 1-0 cikin gasar firimiya lig na Najeriya mako na 13.

Kungiyar Enyimba FC tace babu wani lokaci da shugabanninta suka amince, suka fara, ko aiwatar da wani rage albashi, na yan wasanta ba.

“Wannan rahoton wani abu ne kawai na tunanin marubucin kuma ya kamata jama’a su yi watsi da shi.” inji Enyimba.

Kungiyar ta nuna damuwa cewa irin wannan labarin karya ya fito ne daga wata kafar yada labarai da ake kyautata zaton ba tare da wani yunkurin tabbatar da sahihanci daga kungiyar ko ta hanyar shugabanninta ko kafofin watsa labaranta ba.

Kungiyar Enyimba FC, na goyon bayan girmama juna da kafofin watsa labarai da suka dade suna yi, ta ci gaba da mayar da hankali kan komawa ga hanyoyin nasara.

“Za mu ci gaba da yin aiki kafada da kafada da abokan hulɗar kafofin watsa labarai, don haskaka ayyukanmu da kuma ba da gudummawa ga ci gaban NPFL da ci gaban ƙwallon ƙafa a Najeriya.”

Hukumar shirya gasar cin kofin (NNL) a Najeriya ta tabbatar da janyewar ƙungiyar kwallon kafa ta Dakkada FC da ke Uyo daga gasar NNL26 mai zuwa.

“Hukumar ta yi alƙawarin daidaita jadawalin wasannin domin samar da hanyoyin da za a bi wajen cimma burin da aka sa a gaba. Hakan ya zama dole saboda janyewar ƙungiyar DAKKADA FC daga gasar.” Inji Hukumar.

DAGA KASAR GHANA:

Wani mamba a hukumar kula da wasan kwallon kafa ta kasar Ghana (GFA) Frederick Acheampong, ya ziyarci magoya bayan kulub din Aduana FC da suka ji rauni a wani hatsari a kan hanyarsu ta dawowa gida, bayan wasan GPL da su kayi da ƙungiyar kwallon kafar Asante Kotoko a Kumasi.

Hatsarin da ya jawo harda rasa rayuka. Frederick ya mika ta’aziyya ga iyalai da duk masoyan magoya bayan biyu da suka rasa rayukansu a hatsarin.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/11/RAHOTON-WASANNI-DARE-19-11-2025.mp3
Wasanni

Post navigation

Previous Post: An Gudanar Da Taron Matasan Kasashe 6, Don Kawo Karshen Ta’addanci
Next Post: Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz

Karin Labarai Masu Alaka

An Gudanar Da Taron Matasan Kasashe 6, Don Kawo Karshen Ta’addanci Wasanni
Manya-Manyan Wasannin Wannan Makon Wasanni
Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025. Wasanni
An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe Labarai
Wikki Tourists FC: Ta Yi Sabbin ‘Yan Wasa Uku Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Jagoran Addinin Kirista A Kaduna Ya Rabawa Fiye Da Musulmai Dubu Kayan Abincin Azumi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Alhamis 11.20.2025 Rediyo
  • AFCON 2025, Jerin Abubuwan Da Aka Haramta Wa Magoya Baya Wasanni
  • Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
  • Amurka Ta Bada Tabbacin Baiwa Ukraine Tsaron Na Shekaru 15 Amurka
  • Birtaniya Ta Bukaci Israela Ta Janye Shawarar Fadada Iko Da Kogin Jordan Labarai
  • Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC Najeriya
  • Kasar Amurka Takara Saka Takunkumi Akan Kasar Venezuela Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.