Kungiyar Gwamnonin Arewacin Najeriya, karkashin jagorancin Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ta yi Ala-wadai da harin bama-bamai da ya auku a birnin Maiduguri na jihar Borno, wanda ya yi sanadin asarar rayuka da jikkatar mutane da dama.
A cikin wata sanarwa da aka fitar ta bakin shugaban kungiyar, Inuwa Yahaya, gwamnonin sun bayyana harin a matsayin abin takaici da kuma babbar barazana ga zaman lafiya da tsaron al’umma a yankin Arewa maso Gabas. Sun jajantawa gwamnatin jihar Borno da iyalan wadanda abin ya shafa, tare da addu’ar Allah ya jikansu da rahama, ya kuma bai wa wadanda suka jikkata lafiya.
Kungiyar ta bukaci hukumomin tsaro da su kara kaimi wajen bincike domin gano wadanda ke da hannu a harin, tare da tabbatar da an hukunta su bisa doka.
Haka zalika, sun jaddada bukatar daukar matakan gaggawa domin kawo karshen irin wadannan hare-hare, tare da karfafa tsaro musamman a wuraren taruwar jama’a.
Gwamnonin sun kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta kara tallafawa rundunonin tsaro da kayan aiki na zamani, da kuma inganta hadin gwiwa tsakanin jami’an tsaro da al’umma domin dakile ayyukan ta’addanci a fadin yankin.


