Gwamman kwararru a fannin dokokin kasa da kasa a Amurka sun sa hannun kan budaddiyar wasika dake cewa harin da Amurka ta kaiwa Iran zai iya zama laifi na karya dokar yaki, bayan da shugaba Donald Trump ya jaddada barazanar sa a wannan makon na kai hari kan cibiyar makamashi, da cibiyar tace ruwan sha ta Iran.
Fiye da kwararru 100 a fannin dokokin kasa da kasa a Amurka, ciki har da wadanda suka fito daga manyan jami’o’i kamar su Havard, Yale, Stanford, da jami’ar Califronia, sun bayyana a wasikar da aka wallafa a ranar Alhamis cewa a abinda dakarun Amurka ke aikatawa, da furucin da manyan jami’an ta ke yi, akwai damuwa kwarai na cewa An karya dokar kasa da kasa na kare hakkin dan adam, da kuma dokokin agaji, ciki har da karya dokokin yaki.
Wasikar musamman ta lura da furucin da Trump yayi a tsakiyar watan Maris, inda yace Amurka zata kaiwa Iran hari don jin dadi kawai. Ta kuma ambaci furuci daga sakataren tsaron Amurka Pete Hegseth a farkon watan Maris inda yace America bata bin sakarkarun dokokin yaki.
Kwarrarun sun nuna damuwar su kwarai kan hare-hare da aka kai kan makarantu, wuraren kiwon lafiya da gidaje.


