Farin da ya addabi kasar Kenya tun shekarar 2022, yanzu ya yi tsamari, har ya kai ka yankunan da suke da yalwar ruwa.
Wannan farin ya sa makiyaya cikin mawuyacin hali, inda suka yi asararar dabbobin su da dama, sakamakon rashin wadatacciyyar ciyawa da ruwan sha.
Maria Katanga ‘yar kabilar Masaai, da yawanci suka dogara da kiwon dabbobi don samun abun dogaro, ta shaidawa manema labarai cewa, tun daga watan Agustan bara zuwa yanzu sun yi asarar shanu fiye da 100, da awaki 300 saboda fari, kuma dabbobin da suka rage musu duk sun konjame, ta yadda baza su iya samar da madara ba. Wannan kuma ya sa farashin shanun shima ya ragu.
Yanzu saniyar da ake saidawa shilling 60000 zuwa 70000 na kudin Kenya ya dawo shilling 5000.


