Mataimakin Shugaban Amurka JD Vance ya yi mu’amala da wasu wakilai ta hanyar masu shiga tsakani daga ƙasar Pakistan game da rikicin Iran har zuwa ranar Talata, a cewar wani mutum da ke da masaniya game da lamarin wanda ya shaida wa Reuters. Wannan na nuna yadda rawarsa ke ƙara faɗaɗa wajen ƙoƙarin samar da mafita don kawo ƙarshen rikicin.
Bisa umarnin Shugaba Donald Trump, Vance ya aika da saƙo a ɓoye cewa Trump yana buɗe ƙofa ga tsagaita wuta muddin an cika wasu buƙatun Amurka, kamar yadda majiyar ta shaida wa Reuters a ranar Laraba.
Haka kuma Vance ya isar da abin da majiyar ta bayyana a matsayin “saƙo mai tsauri,” inda ya nuna cewa Trump ya fara gajiya da jinkiri, tare da gargadin cewa za a ƙara matsa lamba kan muhimman ababen more rayuwa na Iran idan Tehran ba ta amince da yarjejeniyar ba.
Majiyar ta ƙara da cewa ƙasar Pakistan na taka rawa a matsayin mai shiga tsakani tsakanin Amurka da Iran.
Vance na taka muhimiyar rawa wajen ƙoƙarin tattaunawa domin kawo ƙarshen yaƙin, wanda yanzu ya shiga mako na biyar.
Ana kallon sa a matsayin wanda zai iya gadan Trump a zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2028, kuma ya ɗauki matakin taka-tsantsan game da rikicin, wanda ya dace da ra’ayinsa na dogon lokaci na nuna shakku kan tsawaita shiga harkokin sojan Amurka a ƙasashen waje.


