Mutane goma sha uku sun mutu, yayin da wasu 57 suka jikkata sakamakon fashewar wasu ababe fashewa sanadiyyar matsalar wutar lantarki a wani sansanin sojoji na ƙasar Burundi a daren Talata, kamar yadda rundunar sojin ƙasar ta bayyana.
Mai magana da yawun sojojin Burundi, Gaspard Baratuza, ya shaida wa taron manema labarai a jiya Laraba cewa gidaje, gine-gine, motoci da kayan aikin soja sun lalace a sakamakon fashewar rumbun ajiyar makamai a Bujumbura, cibiyar kasuwancin ƙasar.
Wani mazaunin Bujumbura da ke zaune kusa da wurin yace fashe-fashen sun ɗauki sa’o’i da dama suna ci gaba.
Ya ce, “An shafe kusan sa’o’i shida ana ganin harsasai suna shawagi a sama suna sauka a wurare daban-daban.” Ya ƙara da cewa, “Mun dai tsaya a inda muke muna fakewa domin tsira,” kamar yadda ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters, inda ya nemi a sakaya sunansa.
A unguwar Musaga da ke kusa da sansanin sojin, wani mazauni ya ce ya ga wata budurwa ta faɗi ƙasa yayin da take gudu tare da wasu mutane. “Bayan ɗan lokaci ne na fahimci cewa bam ya bugi jikin ta da ƙarfi,” in ji shi, shi ma ya nemi a ɓoye sunansa.
Wani mutum kuma ya mutu jim kaɗan bayan an kammala taron addu’a a wata coci a unguwar Gasekebuye, kamar yadda wani mazaunin yankin ya bayyana.


