Zamu bi Sabbin Hanyoyin kara Bunkasa kwallon raga ta badminton a Najeriya Domin samar da aikinyi a tsakanin matasan mu.
Sabon shugaban kungiyar ta kwallon badminton a shiyar jihohin arewa maso tsakiyar Najeriya Alhaji Umma kolo shine ya bayyana a zantawa da Manema Labarai a birnin Minna Fadar Gwamnatin jihar Nejan Najeriya.

Alhaji Umma kolo wanda aka zaba a karshen makon jiya bayan gudanar da wani Babban Taron su na kasa da ya gudana a Birnin Jos ta jihar filato Yace idan matasa suka maida hankali wajan harkar wasanni to tabbas zasu zamo masu dogaro da kai harma su dauki nauyin wasu.
Da yake Karin haske akan salon Shugaban cinsu yace suna da dabaru Masu karfi da wasan kwallon ragar zatayi daraja kamar ta kwallon kafa.
Daga Minna Ga Rahoton Wakilin GTA Hausa Amurka Ke Magana Mustapha Nasiru Batsari


