Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi
Published: February 7, 2026 at 8:33 AM | By: Bala Hassan | Updated: February 7, 2026

Hukumar Kula da Ci Gaban Arewa maso Gabas (NEDC) a tarayyar Najeriya ta nuna matukar tausayawa tare da bayar da cikakken goyon baya ga ‘yan jarida da suka samu raunuka a hatsarin mota yayin da suke bayar da rahoto kan kaddamar da ayyukanta a Jihar Bauchi a ranar Juma’a.

Lamarin ya faru ne lokacin da wata mota dauke da ‘yan jarida 13 daga kafofin watsa labarai daban-daban ta yi hatsari a kan titin Yashi-Yelwan Duguri a karamar hukumar Alkaleri ta jihar Bauchi.

A cikin wata sanarwa da shugaban ayyukan kamfanoni na hukumar, Abba Musa, ya fitar a ranar Juma’a, hukumar gudanarwa, da ma’aikata ta NEDC ta nuna tausayawarsu ga kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ), musamman reshen jihar Bauchi, da gwamnatin jihar Bauchi kan wannan mummunan lamari.

A cewar sanarwar, hatsarin ya faru ne a ranar 6 ga Fabrairu, 2026, yayin da ‘yan jarida ke raka tawagar hukumar wajen kaddamar da ayyukan da ta kammala a fadin jihar Bauchi.

Hukumar ta kara da bayyana cewa hukumar gudanarwa ta amince da samar da cikakken tallafi da kulawa ga ‘yan jarida da suka ji rauni da kuma taimakawa iyalansu.

Sanarwar ta ƙara da cewa an riga an fara ƙoƙarin tuntuɓar kafofin watsa labarai da iyalan ‘yan jaridar da abin ya shafa.

Hukumar NEDC ta bi sahun al’umma wajen yi wa waɗanda abin ya shafa addu’ar samun sauƙi cikin gaggawa da kuma cikakkiyar lafiya,” in ji sanarwar.

Waɗanda suka ji rauni a lamarin sun haɗa da ‘yan jarida daga Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN), The Guardian da The Nation Newspapers; mai ɗaukar hoto na gidan Talabijin ta Najeriya (NTA); ‘yan jarida da masu ɗaukar hoto daga Channels Television da Arise News; wakilin Afirka Mai Zaman Kanta (AIT); ‘yan jarida biyu daga Rediyon Bauchi (BRC); mai ɗaukar hoto daga Gidan Talabijin na Jihar Bauchi (BATV); mai ɗaukar hoto a Online Media, da kuma direban motar.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Kasar Netherland Ta Mayarwa Masar Mutum Mutumin Tarihi
Next Post: Yohanna YD Buru: Makon Haɗin Kan Addinai Ya Ƙarfafa Ilimin Zaman Lafiya A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ministan Tsaron Najeriya Badaru Yayi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Harin Da Israela Ta Kai Gaza Yayi Ajalin Mutane 27 Da Yara Uku Labarai
Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sheikh Ibrahim Sheikh Dahiru Ya Zamo Khalifan Sheikh Dahiru Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Amurka Zata Tantance Fararen Fata ‘Yan Afirka Ta Kudu Afrika
  • ‘Yan Gudun Hijira A Kasar Libya Suna Fuskantar Cin Zarafi Afrika
  • Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu Wasanni
  • An Kaddamar Da Kwamitin Kwallon Kafa A Tsakanin Masarautun Jihar Gombe Labarai
  • An Bude Gasar Kwallon Kafa Ta Mata A Najeriya NWFL 2025 Wasanni
  • An Gano Wani Kurkukun Sirri Da Ake Azaftar Da Mutane A Kasar Libya Afrika
  • Kasashen Da Suke Kawance Da Amurka Sun Juyawa Trump Baya Afrika
  • Al’ummomin da Ambaliyar Ruwan Mokwa a Jihar Nejan Najeriya ta sharewa gidaje sun Koka. Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.