Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamnan Gombe Ya Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekaru 70, Ya Yi Masa Addu’ar Ƙarin Lafiya Da Tsawon Rai Afrika
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika

Sabuwar Shekarar Musulunci: Shugaban Gwamnonin Arewa Ya Yi Kira Da A Yawaita Addu’o’i Da Haɗin Kai
Published: June 16, 2026 at 9:40 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnan jihar Gombe kuma Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF), Muhammadu Inuwa Yahaya, ya taya al’ummar Musulmi a Jihar Gombe da Najeriya baki ɗaya, har ma da sauran Musulmi a faɗin duniya, murnar shiga sabuwar shekarar Musulunci ta 1448 Bayan Hijira (AH).

A cikin saƙon taya murna da ya fitar domin bikin sabuwar shekarar Hijira, Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana farkon sabuwar shekarar Hijira a matsayin lokaci na sabunta ruhi, yin nazari mai zurfi kan rayuwa da kuma ƙara jajircewa wajen bin koyarwar addini, zaman lafiya, tausayi da yi wa bil’adama hidima.

Gwamnan ya ce sabuwar shekarar Musulunci wata dama ce ga al’ummar Musulmi domin su yi waiwaye kan abubuwan da suka gabata, su ɗauki darussa daga gare su sannan su fuskanci gaba da ƙarin imani, fata da ƙuduri.

Ya ce, “Yayin da muke shiga sabuwar shekarar Hijira, ya kamata mu ƙara rungumar kyawawan ɗabi’u na haƙuri, sadaukarwa, juriya da adalci waɗanda Ma’aiki Mai Tsira Annabi Muhammad (SAW) ya nuna a lokacin Hijira.”

Gwamna Inuwa Yahaya ya buƙaci Musulmi da su yi amfani da wannan wata mai alfarma na Muharram da sauran watannin da ke gaba wajen ƙara yawaita addu’o’i domin samun ɗorewar zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba a Jihar Gombe da Najeriya baki ɗaya.

Har ila yau, ya yi kira da a yi addu’o’i na musamman domin samun wadataccen ruwan sama da kuma nasarar kakar noma, yana mai bayyana fatan cewa sabuwar shekarar za ta zo da ƙarin ci gaba da damammaki ga al’umma.

Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa ya kuma jaddada muhimmancin zaman lafiya tsakanin al’umma, girmama juna da haɗin kai tsakanin kabilu da addinai daban-daban a jihar da ƙasa baki ɗaya, musamman a wannan lokaci da ake fuskantar ƙalubalen tsaro a wasu sassan ƙasar.

Gwamna Inuwa Yahaya ya sake tabbatar da aniyar gwamnatinsa na ci gaba da aiwatar da manufofi da ayyukan raya ƙasa da ke da tasiri kai tsaye ga rayuwar jama’a domin inganta walwala da yanayin rayuwarsu.

Ya kuma buƙaci al’umma da su kasance masu bin doka, masu tsayawa kan koyarwar addini da kuma jajircewa wajen gina al’umma mai zaman lafiya, tsaro da ci gaba.

A ƙarshe, Gwamnan ya roƙi Allah Maɗaukakin Sarki da Ya sanya sabuwar shekarar Musulunci ta kasance mai cike da zaman lafiya, ci gaba da rahama ga jihar Gombe, Arewacin Najeriya da ƙasar baki ɗaya.

Afrika, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Nishadi, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: EU Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Amurka Da Iran
Next Post: Sabuwar Shekarar Musulunci 1448: Kiristoci Sun Yi Murna, Sunyi Kiran Samar Da Hutu Ga Shekarar Musulunci

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Yakarawa Mambobin ASUU Kashi 40 Na Albashi Najeriya
Gwamnatin Kano Ta Rufe Gidajen Bukukuwa Da Shakatawa Labarai
Wasu Muhimman Abubuwa Da Najeriya Ba Zata Manta Da Su Ba A 2025 Labarai
Zabebben Shugaban Hungary Yace Zaidawo Da Tsarin Dimokraɗiyya Afrika
Rundunar Tsaron Haɗin Gwiwa Ta Arewa Maso Gabas Ta Kashe Fiye Da ‘Yan Ta’adda 438 Labarai
Hukumar UBRBDA Ta Fara Raba Kayan Noma A Gombe, Yobe Da Borno Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Alejandro Balde Na Dab Da Komawa Manchester United Daga Barcelona
  • Kocin Newcastle Matthias Ya Ce Lewis Hall Ba Zai Koma Manchester United Ba
  • Dan Wasan Baya Na Chelsea, Disasi, Zai Yi Gwajin Lafiyarsa A Crystal Palace
  • Gwamnan Gombe Ya Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekaru 70, Ya Yi Masa Addu’ar Ƙarin Lafiya Da Tsawon Rai
  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kungiyar Kiristoci Ta Karyata Kubutar Da Mambobin Su A Kaduna Afrika
  • ‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farfesa Inuwa Ja’afaru Yakarbi Ragamar Shugabancin Jami’ar Kashere Labarai
  • Kotu A Abuja Tabawa Goodluck Jonathan Daman Tsayawa Takara Afrika
  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai Wasanni
  • Kasar Morocco Ta Kwashe ‘Yan Kasar Daga Sassan Ambaliyar Ruwa Afrika
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Samun Sakamako Mai Kyau A Tattaunawa Da Amurka Amurka
  • An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.