Shugaban Majalisar Kolin Harkokin addinin Musulunci a Najeriya kuma Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’ad Abubakar III, ya kai ziyara ga Shugaban Kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu a fadar Gwamnati dake Abuja ranar Lahadi.
Mai ba Shugaban Kasa shawara kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a wani sako da ya wallafa a shafin sa na X ranar Lahadin.
A cewar sa, Sarkin Musulmin wanda kuma shi ne Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Musulunci a Najeriya, ya gana da shugaban kasar a Abuja ranar 15 ga Maris.
Sai dai har zuwa lokacin hada wannan rahoto, ba a bayyana cikakkun bayanai kan abin da aka tattauna a ganawar ba.


