Shugaban kasar Djibouti Ismael Omar Guelleh ya sake lashe zaben kasar da aka gudanar a ranar Jumu’a da kaci 97.8 cikin dari na kuri’u, a cewar kafar yada labarai ta kasar a ranar Asabar. Wannan ya bashi damar sake rike ragamar mulkin kasar a karo na shida, inda Zai ci gaba da mulkin da ya shafe shekaru 27 yana kai.
Shugaba Guelle ya sa hotonsa a kafar sada zumunta da kalmar cewa An sake zaben sa.
A watan Oktobar bara ne majalisar kasar ta soke dokar da tace duk wanda ya zarta shekaru 75 ba zai iya tsayawa takara ba, abinda ya bawa Guelle me shekaru 78 damar sake tsayawa takara.


