A ranar Alhamis, shugaban hukumar kwallon kafa ta Senegal Abdoulaye Fall, ya dau alwashin yaki da hukuncin da hukumar kwallon Afirka wato CAF ta Yanke na kwace kofin cin gasar kwallon Afirka daga kasar. Yace a hukumar kwallon kafa ta Senegal bazata yadda ta fadi ba a wannan handama da babakere da aka yi mata, zata dau damarar yaki a hukumce.
Hukumar kwallon kafa ta Senegal ta daukaka kara zuwa kotun sulhu ta wasanni, wato CAS, a ranar Laraba don kalubalantar hukuncin da CAF ta yanke, inda ta bawa kasar Morocco ci da maki 3, ita kuma Senegal ba ko daya.
Lauyoyi sun yi gargadin cewa wannan hukunci zai iya sauya duniyar kwallon kafa, kuma zai kassara tsarin cewa hukuncin alkalin wasa shine hukunci na karshe. Sun ce idan hukumar CAF ta yanke hukuncin kwace kofi daga Senegal, watakila kotuna ne zasu yanke wanda zai ci kwallon kafa na duniya nan gaba, maimakon alkalan wasa a filin kwallo.


