Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugabannin Kasashen Afirka Ta Tsakiya Sun Kamallah Taron Koli
Published: January 23, 2026 at 1:33 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugabannin kasashe dake Afirka ta tsakiya sun kammala taron koli da suka yi tare da bada umarnin a dauki matakai cikin gaggawa domin kawo daidaito ga al’amuran kudi da tattalin arziki na kasashen, domin karfafa su ganin koma baya na tattalin arzikin su, da suka hada da dawo da kudaden kasashen da suke ketare.

Shugabannin kasashen shida, sun amince da adawo da kudaden kasashen da suka samu ta fuskar albarkatun kasa, kamar yadda jawabin bayan taro na musamman da suka yi a birnin Brazaville ya nuna.

Taron kolin wadda aka gudanar karkashin laimar kungiyar raya tattalin arzikin kasashe dake Afirka ta tsakiya, an yi zaman na gaggawa domin tunkarar tafiyar hawainiyar tattalin arzikin yankin, faduwar farashin albarkatun kasa, matsalolin sakewar yanayi, da kuma tsuke bakin aljihu daga hukumomin duniya.

A bara babban bankin kasashe dake yankin Afirka ta tsakkiya, da suka hada da manyan bankunan kasashen Kamaru, da Chadi, da kasar Afirka ta tsakiya,da Gabon, da Kwango, da Equatorial Guinea, sun bukaci kamfanonin hakar mai a yankunan su adana kudaden farfado da muhalli da aka tanadar karkashi asusun babban bankin kasashen da asusun bada lamuni na duniya watau IMF a takaice, yake bada goyon baya, mataki da kamfanonin hakar man basu ji dadi ko amince dashi ba.

Kudaden wadanda kamfanonin mai din suka tanadar domin ayyukan tsabtacewa da farfado da muhalli idan aka gama hakar mai sun kai dala bilyan biyar zuwa 10.

Haka nan shugabannin sun bada umarnin hukumomin kasashen su kammala shirye shirye da yarjejeniya gamda kasafin kudi da tattalin arziki da asusun bada lamuni na duniya IMF.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Tinubu Ya Rantsar Da Shugabar Hukumar FCC
Next Post: Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista

Karin Labarai Masu Alaka

Jama’ar Kasar Iran Sun Bayyana Goyon Baya Ga Ayatollah Mojtaba Khameni Afrika
Farashin Mai Yana Cigaba Da Karuwa Afrika
Sanyin Hunturu Yayi Ajalin ‘Yan Cirani A Morocco Afrika
Malaman Addinin Musulunci Da Kirista Sunyi Bikin Cika Shekara 15 Na Iftar A Najeriya Afrika
Ukraine Zata Sayi Iskar Gas Daga Mozambique Afrika
Kamfanin Jiragen Saman Ethiopia Zai Kafa Babban Filin Jirgi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Rasha Yafara Ganawa Da Jakadun Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Ukraine Amurka
  • Gwamnatin Trump Ta Karawa Iran Wasu Takunkumai Amurka
  • Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kamfanin Jiragen Saman Ethiopia Zai Kafa Babban Filin Jirgi Afrika
  • Kungiyar EU Zata Taimakawa Somalia Da Kudade Labarai
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakoncin Wasannin Afirka Na 2031 Wasanni
  • An Gudanar Da Addu’oi Ga Mutane 16 Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe a Australiya Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.