Shugabannin kasashe dake Afirka ta tsakiya sun kammala taron koli da suka yi tare da bada umarnin a dauki matakai cikin gaggawa domin kawo daidaito ga al’amuran kudi da tattalin arziki na kasashen, domin karfafa su ganin koma baya na tattalin arzikin su, da suka hada da dawo da kudaden kasashen da suke ketare.
Shugabannin kasashen shida, sun amince da adawo da kudaden kasashen da suka samu ta fuskar albarkatun kasa, kamar yadda jawabin bayan taro na musamman da suka yi a birnin Brazaville ya nuna.
Taron kolin wadda aka gudanar karkashin laimar kungiyar raya tattalin arzikin kasashe dake Afirka ta tsakiya, an yi zaman na gaggawa domin tunkarar tafiyar hawainiyar tattalin arzikin yankin, faduwar farashin albarkatun kasa, matsalolin sakewar yanayi, da kuma tsuke bakin aljihu daga hukumomin duniya.
A bara babban bankin kasashe dake yankin Afirka ta tsakkiya, da suka hada da manyan bankunan kasashen Kamaru, da Chadi, da kasar Afirka ta tsakiya,da Gabon, da Kwango, da Equatorial Guinea, sun bukaci kamfanonin hakar mai a yankunan su adana kudaden farfado da muhalli da aka tanadar karkashi asusun babban bankin kasashen da asusun bada lamuni na duniya watau IMF a takaice, yake bada goyon baya, mataki da kamfanonin hakar man basu ji dadi ko amince dashi ba.
Kudaden wadanda kamfanonin mai din suka tanadar domin ayyukan tsabtacewa da farfado da muhalli idan aka gama hakar mai sun kai dala bilyan biyar zuwa 10.
Haka nan shugabannin sun bada umarnin hukumomin kasashen su kammala shirye shirye da yarjejeniya gamda kasafin kudi da tattalin arziki da asusun bada lamuni na duniya IMF.


