A halin da ake ciki, Kasar Spain ta yi kira ga Tarayyar Turai da ta dauki matakan kirkiro rundunar sojojin hadin guiwa ta Kasashen Tarayyar Turai, domin ta zamo hannunka mai sanda ga duk wani mai neman nuna musu yatsa.
Ministan harkokin wajen Spain, Jose Manuel Albares ya fada ranar laraba cewa ya kamata kasashen Turai su fara da hada hancin kayan tsaron da suke da su da hade masana’antunsu na tsaro, kafin su kafa runduna guda.
Albares yace a zahiri ne cewa akwai damuwa a kan ko al’ummar kasashen Turai zasu yarda da kafa runduna guda, amma kuma yace samun runduna guda ta fi tasiri a kan rundunoni har 27 dabam-dabam.
Wannan kira nasa yana zuwa kafin wani taron gaggawa da shugabannin Tarayyar Turai zasu yi ranar alhamis a Brussels domin maida martani bai daya ga barazanar shugaban Amurka Donald Trump na saye ko kwace yankin Greenland.
Wani kakakin majalisar TT ya tabbatar da cewa za a gudanar da wannan taron gaggawa na ranar alhamis duk da cewa shugaba Trump ya fada cewa shi da sakatare janar na NATO, Mark Rutte sun cimma daidaituwa kan yadda za a takali batun na Greenland.
Albares yace ba manufar wannan runduna da yake kiran da a kafa ce ta maye grbin NATO ba, amma kuma akwai bukatar nunawa duniya cewa ba wani wanda zai iya yi ma Turai barazanar soja ko ta tattalin arziki.
Wannan ra’ayi na kafa rundunar sojojin hadin guiwa ta kasashen Turai ba sabon abu ba ne. An fara gabatar da shi tun shekarar 1951 domin tunkarar tsohuwar Tarayyar Soviet da tabbatar da cewa ko kasar Jamus ta sake yin damara ba zata yi barazana ga makwabtanta ba. Majalisar dokokin kasar Faransa ita ce ta kashe wannan yunkurin ta hanyar jefa kuri’ar kin yarda da shi.


