Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Tarayyar Turai Zasu Kirkiro Sojojin Haɗin Gwiwa
Published: January 22, 2026 at 7:45 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 22, 2026

A halin da ake ciki, Kasar Spain ta yi kira ga Tarayyar Turai da ta dauki matakan kirkiro rundunar sojojin hadin guiwa ta Kasashen Tarayyar Turai, domin ta zamo hannunka mai sanda ga duk wani mai neman nuna musu yatsa.

Ministan harkokin wajen Spain, Jose Manuel Albares ya fada ranar laraba cewa ya kamata kasashen Turai su fara da hada hancin kayan tsaron da suke da su da hade masana’antunsu na tsaro, kafin su kafa runduna guda.

Albares yace a zahiri ne cewa akwai damuwa a kan ko al’ummar kasashen Turai zasu yarda da kafa runduna guda, amma kuma yace samun runduna guda ta fi tasiri a kan rundunoni har 27 dabam-dabam.

Wannan kira nasa yana zuwa kafin wani taron gaggawa da shugabannin Tarayyar Turai zasu yi ranar alhamis a Brussels domin maida martani bai daya ga barazanar shugaban Amurka Donald Trump na saye ko kwace yankin Greenland.

Wani kakakin majalisar TT ya tabbatar da cewa za a gudanar da wannan taron gaggawa na ranar alhamis duk da cewa shugaba Trump ya fada cewa shi da sakatare janar na NATO, Mark Rutte sun cimma daidaituwa kan yadda za a takali batun na Greenland.

Albares yace ba manufar wannan runduna da yake kiran da a kafa ce ta maye grbin NATO ba, amma kuma akwai bukatar nunawa duniya cewa ba wani wanda zai iya yi ma Turai barazanar soja ko ta tattalin arziki.

Wannan ra’ayi na kafa rundunar sojojin hadin guiwa ta kasashen Turai ba sabon abu ba ne. An fara gabatar da shi tun shekarar 1951 domin tunkarar tsohuwar Tarayyar Soviet da tabbatar da cewa ko kasar Jamus ta sake yin damara ba zata yi barazana ga makwabtanta ba. Majalisar dokokin kasar Faransa ita ce ta kashe wannan yunkurin ta hanyar jefa kuri’ar kin yarda da shi.

Labarai, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kungiyar Maharba Da ‘Yan Sintiri Sun Samu Kyautar Motoci
Next Post: Boko Haram Sun Farmaki Sansanin Sojoji A Borno

Karin Labarai Masu Alaka

Hukumar Zabe A Najeriya Ta Cigaba Da Rijistar Katin Zabe Labarai
An Yanke Hukuncin Kisa Ga Hasina Tsohuwar Firaiy-Ministan Bangladash Labarai
Masar Ta Jibge Jiragen Yaki Marasa Matuka Afrika
Shugaban Trump: Washington Zatayi Cinikayya Da Indiya Amurka
Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
Ghana Ta Haramta Hakar Ma’adinai A Gandunan Dajin Data Kebe, Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Za’a Dauko Messi Aro Zuwa Barcelona Deco Wasanni
  • An Gano Wasu Boma Bomai Da Aka Binne A Jihar Neja Najeriya
  • Anyi Taho Mugama Tsakanin ‘Yan Sandan Turkiyya Da ‘Yan Kungiyar ISIS Afrika
  • Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
  • Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
  • Umar Aliyu, Shugaban Magoya Bayan Wikki Tourist
    Jagorancin Wikki Tourist FC Na Samun Yabo Wasanni
  • Maharan Bindiga Sun Kashe Mutane 12 Masu Hakar Ma’adanai A Jihar Filato Labarai
  • Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.