Togo ta kama tsohon shugaban kasar Burkina Faso, kuma ta tusa keyarsa zuwa kasar sa, bayan da jami’ai a Ouagadougou suka yi zargin yana kitsa juyin mulki, kamar yada wasu majiyoyi biyu suka fadawa kamfanin dillancin labarai na Reuters ranar talata.
Paul Henri Damiba, ya hau mulki ne a shekara ta 2022 sakamakon juyin mulki da sojoji suka yiwa gwamnatin farar hular kasar, wacce tayi bakin jini saboda yadda ‘yan tawaye masu ikirarin Islama suke tada kayar baya.
Sai dai shi ma Damiba, da ya kasa shawo kan fitinar ‘yan bindigar, lamarin ya harzuka dakarun kasar dake yammacin Afirka, shi ma aka yi masa juyin mulki a cikin shekarar da ya hau mulki, mataki da ya kawo shugabancin Ibrahim Traore, wanda yake ci gaba da mulkin kasar.
A farkon wannan wata, Burkina Faso tace ta wargaza wan yunkurin kashe Troare, da take zargin Damiba da kullawa, wanda yake zaman gudun hijra a Lome babban birnin kasar Togo.
Wata majiya ta fuskar tsaro, da wata majiya kusa da fadar shugaban kasar Togo, sun gayawa Reuters a ranar talata cewa, an kama Damiba, ranar Asabar, kuma an maida shi Burkina Faso.
A dai ranar Talatan gwamnatin kasar Togo ta tabbatar da wannan labari, kuma cikin sanarwar da ta bayar wacce aka rubuta ranar Litinin, sannan aka raba, Damiba, yana fuskantar zargin almubazzaranci da dukiyar al’umma, arzurta kansa ba bisa ka’ida ba, rashawa da kuma halatta kudaden haram, amma sanarwa bata ambaci zargin juyin mulki ba.
Kamfanin dillancn labarai na Reuters, ya kasa magana da Damiba, kuma babu tabbas ko yana da lauya a Togo. Gwamnatin Burkina Faso, bata maida martani ba da aka nemi jin ta bakinta.


