Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Togo Ta Kama Tsohon Shugaban Kasar Burkina Faso Saboda Kitsa Juyin Mulki
Published: January 20, 2026 at 8:09 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Togo ta kama tsohon shugaban kasar Burkina Faso, kuma ta tusa keyarsa zuwa kasar sa, bayan da jami’ai a Ouagadougou suka yi zargin yana kitsa juyin mulki, kamar yada wasu majiyoyi biyu suka fadawa kamfanin dillancin labarai na Reuters ranar talata.

Paul Henri Damiba, ya hau mulki ne a shekara ta 2022 sakamakon juyin mulki da sojoji suka yiwa gwamnatin farar hular kasar, wacce tayi bakin jini saboda yadda ‘yan tawaye masu ikirarin Islama suke tada kayar baya.

Sai dai shi ma Damiba, da ya kasa shawo kan fitinar ‘yan bindigar, lamarin ya harzuka dakarun kasar dake yammacin Afirka, shi ma aka yi masa juyin mulki a cikin shekarar da ya hau mulki, mataki da ya kawo shugabancin Ibrahim Traore, wanda yake ci gaba da mulkin kasar.

A farkon wannan wata, Burkina Faso tace ta wargaza wan yunkurin kashe Troare, da take zargin Damiba da kullawa, wanda yake zaman gudun hijra a Lome babban birnin kasar Togo.

Wata majiya ta fuskar tsaro, da wata majiya kusa da fadar shugaban kasar Togo, sun gayawa Reuters a ranar talata cewa, an kama Damiba, ranar Asabar, kuma an maida shi Burkina Faso.

A dai ranar Talatan gwamnatin kasar Togo ta tabbatar da wannan labari, kuma cikin sanarwar da ta bayar wacce aka rubuta ranar Litinin, sannan aka raba, Damiba, yana fuskantar zargin almubazzaranci da dukiyar al’umma, arzurta kansa ba bisa ka’ida ba, rashawa da kuma halatta kudaden haram, amma sanarwa bata ambaci zargin juyin mulki ba.

Kamfanin dillancn labarai na Reuters, ya kasa magana da Damiba, kuma babu tabbas ko yana da lauya a Togo. Gwamnatin Burkina Faso, bata maida martani ba da aka nemi jin ta bakinta.

Afrika, Siyasa

Post navigation

Previous Post: Tsohon Shugaban Kasa Obasanjo Ya Ziyarci IBB
Next Post: Sojojin Kasar Uganda Sun Bazama Neman Bobi Wine Sakamakon Rikicin Bayan Zabe

Karin Labarai Masu Alaka

Ministan Sadarwan Kasar Uganda Yayi Allah Wadai Da Kaiwa Bobi Wine Hari Afrika
Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum Afrika
Kamfanin Bitcoin A Korea Ta Kudu Yayi Kuskuren Turawa Masu Mu’amala Da Kamfanin Kudade Afrika
An Kashe Sojojin Ukraine Dubu 55 A Kasar Rasha Afrika
Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet
  • Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado
  • Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia
  • Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi Tsaro
  • Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki Najeriya
  • Sabon Jadawalin Gasar Kwalon Kafa Ta Turai 2026 Wasanni
  • Rundunar Tsaro Suna Cigaba Da Nasara Akan ‘Yan Ta’adda Tsaro
  • Jamhuriyar Nijar Ta Fitar Da Doka Domin Kare ‘Yancin ‘Yan Kasar Tsaro
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Yi Ma Wasu Mutane Yankan Rago A Jihar Neja Labarai
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet Labarai
  • Umar Ya Lashe Kyautar Gwarzon ‘Dan-Wasa Na 2025 Wasanni
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.