Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Trump Yace Amurka Ta Kai Hare-Hare Masu Yawa Akan ‘Yan Ta’adda A Najeriya
Published: December 26, 2025 at 5:03 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Trump ya ce Amurka ta kai “hare-hare masu yawa” masu kisa kan ‘yan ta’adda a Najeriya.

Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya ce a ranar Alhamis sojojin Amurka sun kai munanan hare-hare kan ‘yan ta’addar Daular Musulunci (ISIS) a Arewa maso Yammacin Najeriya, tare da yin barazanar ci gaba da kai hare-hare idan ‘yan ta’addan suka ci gaba da kashe kiristoci.

Shugaban ya bayyana hakan ne a shafinsa na X inda ya ƙara da cewa Ma’aikatar Yaƙi ta Amurka ta aiwatar da hare-hare masu nasara da dama.

Ya rubuta cewa, “Yau da daddare, bisa umarni na a matsayi na na Babban Kwamandan Sojojin Amurka ta kaddamar da wani mummunan hari mai ƙarfi kan ‘yan ta’addar ISIS a Arewa maso Yammacin Najeriya, waɗanda suka dade suna kai hari tare da kashe Kiristoci marasa laifi.

“A baya na yi gargaɗi ga waɗannan ‘yan ta’adda cewa idan ba su daina kisan Kiristoci ba, za su fuskanci mummunan sakamako, kuma a daren yau hakan ta faru.

“Ma’aikatar Yaƙi ta aiwatar da hare-hare masu tsari da nagarta da dama, irin waɗanda Amurka kaɗai ke iya aiwatarwa.

“A ƙarƙashin jagoranci na, ƙasar mu ba za ta bari ta’addancin Musulunci mai tsatsauran ra’ayi ya bunƙasa ba.

“Allah Ya albarkaci sojojin mu, kuma Barka da kirsimeti ga kowa, har da ‘yan ta’addar da aka kashe, waɗanda za su ƙaru idan suka ci gaba da kisan Kiristoci.”

Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya
Next Post: Jamhuriyar Nijar Ta Dakatar Da Bawa Amurkawa Visa

Karin Labarai Masu Alaka

Trump Yayi Barazanar Goyon Bayan Hari Akan Kasar Iran Labarai
Shugaba Tinubu Ya Turawa Majalisa Sunayen Mutane Biyun Da Zasu Shugabanci Sashin Albarkatun Mai Labarai
Gwamnan Neja Bago Na Cin Zarafin Talakawan Da Suka Zabe Shi Labarai
Maharan Bindiga Sun Kashe Mutane 12 Masu Hakar Ma’adanai A Jihar Filato Labarai
An Gudanar Da Jana’izar ’Yan Jaridan Da Suka Rasu A Jihar Gombe Labarai
Akwai Bukatar Bincikar Umurnin Da Sakataren Tsaro Pete Ya Bada Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • AFCON ChelIe, Ya Fidda Sunayen ‘Yan Wasan Super Eagles Na Karshe. Wasanni
  • Bahagon Mancha Ya Buge Bahagon Maitakwasara Da Wasun Su! Nishadi
  • Gwamnatin Tarayya Na Kokarin Hana Demokraɗiyya A Najeriya Siyasa
  • Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade Najeriya
  • Iran Ta Kama Wani Jirgin Ruwa Shake Da Mai Labarai
  • Sakataren Gwamnatin Amurka Ya Bayyana Bawa Kungiyoyin Agaji Damar Kai Taimako Sudan Amurka
  • Najeriya, Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Sama Da 80, Sun Ceto 34 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hukumar CAC Zata Dakatar da POS Mara Rijista a Kasar Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.