Ranar talata, wakilan majalisar dokokin Phillipines suka yi zama domin yanke shawarar ko su ci gaba da sauraron karar neman tsige shugaban kasar Ferdinad Marcos Jr., wanda ake zargi da cin amanar kasa, rashawa, da kuma keta tsarin mulkin kasar.
Shugaba Marcos wanda yake tsakiyar wa’adin mulkinsa na shekaru shida, wanda ya musanta zargin, yana Fuskantar tuhuma da wani lauya dan gwagarmaya ya shigar gaban majalisar.
Idan har majalisa ta amince da zargin da ake yi wa shugaba Marcos, zai kasance shugaban kasar Phillipines na biyu da za’a tsige, na farko shine shugaba Joseph Estrada, wanda shari’arsa a shekara ta 2001 ta wargaje lokacin da wasu masu gabatar da kara suka fice daga inda ake shari’ar.
Laifuffukan da lauyan yake zargin shugaban na Phillipines sun hada da laifin sa a kama tsohon shugaban kasar Rodrigo Dutarte da mika shi ga kotun kasa da kasa mai hukunta manyan laifuffuka kan zargin da kotun take yi wa Dutarte na kashe duban mutane lokacin mulkinsa karkashin shirin yaki da miyagun kwayoyi.
Haka nan Marcos yana Fuskantar zarginsa kan yadda aka kashe dukiyar al’umma da ya kai ga abun fallasa kan ayyukan kare jama’a daga bala’in ambaliyar ruwa, da kuma zargin da ake yiwa shugaban kasar na mafani da miyagun kwayoyi, wadda idan ya tabbata ba zai cancanci ci gaba da shugabancin kasar ba.


