A Najeriya akalla mutane 25 ne aka kashe sakamakon wani harin da ‘yan bindiga da ake kyautata zaton mayakan Boko Haram suka kai kan wani gari, a arewa maso gabashin kasar kamar yadda ‘yan uwan wadanda harin ya rutsa da su suka fada.
Wadanda suka halaka a harin leburori ne wadanda suka yi balaguro zuwa Sabon Gari a jihar Borno domin aiki a wani wuri da ake gine gine, sai ‘yan bindiga suka kutsa cikin gari ranar Alhams suka bude wuta, kamar yadda ‘yan uwan wadanda harin ya rutsa da su, Hassan Usman, da Auwal Isa suka fada.
Dan majalisar dattawan Najeriya mai wakiltar ‘yankin, Senata Ali Ndume, yace ya kadu, kuma yayi bakin cikin kashe mutane a yankin da yake wakilta.
Idan masu sauraro zasu iya tunawa a wani hari na daban da mayakan saka kai a ranar Alhamis a Sabon Garin, sun kashe sojoji kasar 9, da dakarun JTF 2, lokacin da suka farwa wani sansanin sojoji da asubahi, wasu 16 suka jikkata.
Jihar Borno, inda mayakan Boko Haram da reshen ISIS da aka fi sani da ISWAP suka zafafa kaihare hare kan jerin gwanonin sojoji da farar hula, har yanzu nanne cibiyar tada kayar bayan da mayakan suke yi na tsawon shekara 17 yanzu.


