Yakin da ake yi a gabas ta tsakiya, ya rage jigilar nama da kenya take sayarwa kasashe dake yankin da kamar kashi biyar, musamman a dai dai wannan lokaci na azumin watan Ramadan, ganin karin kudin jigilar nama ta sama ya dakatar aikin, kamar yadda jami’ai a wannan masana’natar suka gayawa kamfanin dillancin labarai na Reuters.
Kasashe dake gabas ta tsakiya sune manyan kasuwar nama daga Kenya, inda hadaddiyar daular larabawa take sayen kashi 40-60 na nama daga kasar, kamar yadda shugaban Kungiyar masu cinikin naman dabbobi da kaji na kenya Nicolas Ngahu ya fada.
A wani gefe kuma, kenyan ta kama wani mutum yana shirin shigo da wasu halittu dangin kiyashi cikin kasar.


