Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027 Afrika
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin Afrika
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta Afrika
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe Afrika
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo Afrika

Yobe Ta Sake Jaddada Ƙudirin Rage Mutuwar Yara
Published: July 7, 2026 at 6:44 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Yobe dake arewa maso Gabashin Najeriya ta sake jaddada aniyarta na rage yawan mutuwar yara masu ƙasa da shekara biyar ta hanyar ci gaba da aiwatar da shirin SARMAAN, tare da shirye-shiryen faɗaɗa shi zuwa dukkan ƙananan hukumomi 17 na jihar.

Ana gudanar da shirin ne na haɗin gwiwa da African Field Epidemiology Network (AFENET) Nigeria, inda aka faɗaɗa shi daga ƙananan hukumomi 10 a matakin farko zuwa 13 a zagayen da ake gudanarwa a halin yanzu.

Babban Jami’in Hulɗa da Gwamna kan Kula da Lafiya a Matakin Farko, Dakta Umar Ciroma, ya ce shirin ya samo asali ne daga shawarar Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ga ƙasashen da ke fama da yawan mutuwar yara masu ƙasa da shekara biyar.

Ya bayyana cewa ana bai wa yara ƙwayar maganin Azithromycin sau shida cikin tsawon shekaru uku, ana ba su duk bayan watanni shida, domin kariya daga wasu cututtukan ƙwayoyin bacteria da ke haddasa ciwon huhu, cutar sepsis, cututtukan fata, trachoma da kuma wasu nau’ikan gudawa.

Al’ummomi da dama a faɗin jihar sun ci gaba da karɓar shirin hannu bibbiyu, inda iyaye da masu kula da yara suka bayyana cewa sun lura da ingantuwar lafiyar yaransu bayan karɓar maganin.

Haka kuma, Cibiyar Binciken Lafiya ta Najeriya (NIMR) na sa ido tare da tantance tasirin shirin wajen tabbatar da cewa duk wani mataki na gaba zai kasance bisa hujjojin kimiyya.

Masu ruwa da tsaki sun ce haɗin gwiwar gwamnati, ma’aikatan lafiya, abokan hulɗar ci gaba da al’ummomi na ƙara wa jama’a kwarin gwiwa kan shirin, tare da ƙarfafa ƙoƙarin rage mutuwar yara da za a iya kauce wa a jihar Yobe.

Afrika, Kimiya, Kiwon Lafiya, Labarai, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Rundunar ‘Yan Sandan Kebbi Ta Dakile Yunkurin Garkuwa Da Mutune, Ta Kama Masu Laifi
Next Post: ‘Yan Sandan Bauchi Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Fashi da Makami A Gadau

Karin Labarai Masu Alaka

Mayakan Boko Haram Da ISWAP Sun Kai Hari Cikin Dare Afrika
Kasar Kenya Zata Samar Da Makamashi Labarai
Kotun Daukaka Kara A Faransa Zata Tabbatar Da Hukuncin ‘Yan Jam’iyyar Ra’ayin Rikau Labarai
Kotun Tarayya Tabada Belin Nasiru El Rufai Afrika
Isra’ila Ta Zantar Da Hukuncin Kisa Ga Masu Kai Hare Hare Labarai
‘Yan Kungiyar Boko Haram Sun Yi Awon Gaba Da Mata 13 A Borno Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • APC: Tinubu Da Shettima Za Su Sake Neman Wa’adi Na Biyu A 2027
  • Sabuwar Sakatariyar Ƙungiyar Gwamnonin Arewa Za Ta Ƙarfafa Ayyukan Ci Gaban Yankin
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta
  • Gobara Ta Lalata Babban Zauren Majami’ar ECWA Gospel A Gombe
  • Gombe: ‘Yan Sanda Sun Tarwatsa Ƙungiyar Masu Fashi Da Damfara Ta Yanar Gizo

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Magoya Bayan Obi Sun Yi Tutsu Gabanin Zaben 2027 Siyasa
  • Shugaban Amurka Yace Zasu Kakabawa Mashigar Hormuz Takunkumi Afrika
  • Shugaba Tinubu Zai Kara Karbo Bashin Dala Miliyan 516 Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Iran Ta Kai Hari Matatar Mai A Kuwait Afrika
  • Hanyar Gombe Dukku Darazo Ta Zamo Abun Damuwa Ga Al’ummar Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • Tinubu Na Kokarin Rage Tsadar Sufuri Ta Hanyar Shirin CNG Afrika
  • ‘Yan Kasar Cuba Sunyi Zanga Zanga A Ofishin Jakadancin Amurka Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.