Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji
Published: December 7, 2025 at 3:30 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 7, 2025

Ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen Afirka ta Yamma Ecowas ta ce a shirye take ta taimaka wa Jamhuriyar Benin da sojoji domin daƙile juyin mulkin da wasu sojoji suka yi iƙirarin yi.

Matakin na Ecowas na zuwa ne bayan wani rukunin soji sun sanar da kifar da gwamnatin Shugaba Patrice Talon a kafar talabijin ɗin ƙasar a ranar Lahadi tare da kafa gwamnatin riƙon ƙwarya.

Wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar ta ce ta ɗora wa sojojin alhakin “duk wani rai da aka rasa” sakamakon yunƙurin nasu.

“Ecowas za ta taimaka wa gwamnati da al’umma da duk abin da ya kamata, ciki har da aika dakarun ko ta kwana domin kare tsarin mulki da kuma ‘yancin Benin,” a cewar sanarwar da hukumar Ecowas mai hedikwata a Abuja ta fitar

Sai dai hukumomi a ƙasar sun ce sun shawo kan lamurra bayan yunƙurin juyin mulkin.

“An shawo kan lamarin sannan mafi yawan rundunar soja na goya wa shugaban ƙasa baya haja kuma muna ƙara shawo kan al’amuran.” kamar yadda Ministan harkokin waje Shegun Adjadi Bakari ya faɗa wa kamfanin labarai na Reuters.

Afrika

Post navigation

Previous Post: An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin
Next Post: ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery

Karin Labarai Masu Alaka

Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala Afrika
Hawan Durba A Fadar Sarkin Zazzau Afrika
An Zargi Babban Mai Gabatar Da Kara A Kotun Duniya Ta ICC Afrika
Kungiyar Kiristoci Ta Karyata Kubutar Da Mambobin Su A Kaduna Afrika
Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato Afrika
Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke Amurka
  • Mayakan RSF Sun Zafafa Kai Hare Hare Da Jirgi Maras Matuki A Sudan Labarai
  • Hukumar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Jama’ar Jos Ta Arewa Su Rika Bin Doka Afrika
  • Magoya Bayan Nice Sun Kai Hari Wa ‘Yan Wasansu Wasanni
  • Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
  • Hotunan Hawan Sallah A Masarautar Bauchi Afrika
  • Iran Tayi Allah Wadai Da Kai Hari Cibiyar Pars Afrika
  • Zulum Ya Rushe Majalisar Zartarwa Ta Jihar Borno Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.