Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Da Arzikin Mu: Bamu Ba Bautawa Turawan Yamma
Published: December 8, 2025 at 4:42 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

A karon farko tun bayan da gwamnatin Nijar ta kudiri aniyar maka kamfanin Orano a kotu, kungiyoyin farar hula a kasar sun jaddada goyon baya kan abin da suka kira yunkurin kwato ‘yancin a kan sha’anin ma’adanai.
Kungiyoyin sun kuma shawarci hukumomin na Nijar da su janye lasisin hakar zinare daga hannun kamfanonin da suka yi kaka-gida don mayar da komai a hannun ‘yan kasa.
A wata sanarwar da ta fitar ne kungiyar M62 ta bayyana matsayinta dangane da kace nacen da ya taso a tsakanin hukumomin Nijar, da kamfanin Orano na Faransa bayan da Nijar ta fara kwashe ton ton na Uranium din da ke jibge shekaru sama da biyu a garin Arlit.
Kungiyar tace ta na goyon matakin da gwamnatin Nijar ta dauka, wanda ta ke ganinsa tamkar matakin kawo karshen mulkin mallakar da aka shafe shekaru fiye da 60 a na yi wa kasar harakar Uranium. Falmata Taya na daga cikin shugabanin M62.
Ita ma kungiyar FRSA mai da’awar kwato ‘yancin kai Afirka a sanarwar da ta bayar ta bayyana gamsuwa da abin da ta kira sabon babin da gwamnatin Abdourahamane Tiani ta bude a fannin ma’adanan karkashin kasa. Salissou Ibrahim shine sakataren watsa labaran kungiyar.
Ko baya ga harakar Uranium kungiyar M62 na ganin bukatar gwamnatin Nijar ta fadada sauye sauyen da ta fara zuwa sha’anin hakar zinare.
Mahawwara kan hurumin fitar da Uranium zuwa waje a tsakanin gwamnatin Nijar da kamfanin Orano na Faransa na ci gaba da karfafa ne a wani lokacin da bangarorin biyu ke jiran hukuncin kotun CIRDI dangane da makomar ton 1300 na Uranium da ke girke a yankin arewacin Nijar.
M62 ta bukaci hukumomin kasar su gudanar da bincike kan illahirin aiyukan bankin duniya saboda alakarsu da kotun CIRDI.
Afrika

Post navigation

Previous Post: An Saka Dokar Hana Fita A Karamar Hukumar Lamurde Jihar Adamawa
Next Post: “Hotuna” An Sako Daliban Makarantar St. Mary’s Su 100

Karin Labarai Masu Alaka

Iran Zata Kai Hari Tashar Makamashin Ruwa A Gulf Afrika
Mabiya Dariqar Tijjaniyya Sunfara Gudanar Da Addu’oi Saboda Tsare Sheikh Sani Khalifa Zariya Afrika
Fargaba Ta Karu Duk Da Tsagaita Wuta Tsakanin Iran Da Amurka Afrika
Majalisar Dokokin Kamaru Ta Amince Da Wasu Sauye Sauye Afrika
Asusun IMF Zasu Ziyarci Kasar Gabon Afrika
Harin Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Kakakin ‘Yan Tawayen M23 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa
  • Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Jarida Sunyi Mummunan Hatsari A Bauchi Labarai
  • Shugaban Koriya Ta Arewa Ya Gabatar Da Gwajin Makami Mai Linzami Afrika
  • Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
  • Zulum Ya Rushe Majalisar Zartarwa Ta Jihar Borno Afrika
  • Kamfanin Magani Na Aspen Yayi Gagarumar Asara A Cinikayya Afrika
  • An Kubutar Da Wani Wanda Mahaifinsa Ya daure Da Sarka Tsawon Shekaru 17 A Bauchi Labarai
  • ‘Yan-Ta’adda Sun Yi Ma Wasu Mutane Yankan Rago A Jihar Neja Labarai
  • Kungiyar MDD Ta Bukaci Ayi Bincike Game Da Kashe ‘Yan Iran Sauran Duniya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.