Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya
Published: December 11, 2025 at 6:49 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kwamitocin Kasafin Kuɗi na Majalisar Dokokin Amurka sun jaddada kudirin Amurka na tunkarar take-taken addini a duniya, musamman a Najeriya.

Wannan na zuwa ne bayan ziyarar tawagar ‘yan majalisar da Shugaba Donald Trump ya tura ƙarƙashin jagorancin Riley Moore.

A Najeriya, tawagar ta gana da mai bawa Shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, domin ƙarfafa haɗin gwiwar yaki da ta’addanci da tsaro a yankin.

Moore ya kai ziyara Benue, inda ya gana da shugabannin Katolika da na al’ummar Tiv tare da duba sansanonin ‘yan gudun hijira.

Ya bayyana abin da ya gani a matsayin abin tausayi, inda ya ruwaito tashin hankali da kisan gilla da suka tilasta dubban Kiristoci tserewa daga gidajen su.

Ya ce fiye da Kiristoci 600,000 na rayuwa a sansanonin ‘yan gudun hijira a Benue. Moore ya kuma yi zargin “harin kisan kare dangi da Fulani suke yi a jihar.

Tawagar ta yaba wa gwamnatin Najeriya kan ceto daliban makarantar Katolika fiye da 100, tare da cewa ƙawancen tsaro tsakanin Najeriya da Amurka ya fara inganta, amma akwai sauran aikin da za a yi.

Ziyarar ta zo ne a daidai lokacin da dangantaka ke ƙara tsami bayan gwamnatin Trump ta sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake zargin suna keta ‘yancin addini, matakin da ya haddasa ce-ce ku-ce a bangaren diplomasiya.

Gwamnatin Tarayya ta ce ba a nuna bambanci ga addini, saboda rashin tsaro yana shafar kowa.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar
Next Post: Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa

Karin Labarai Masu Alaka

CBN: An Samu Ƙaruwar Masu Cin Bashin Banki Basa Biya Najeriya
Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
Hukumar NDLEA Ta Kama Wata Mata Da cikin Bogi Na ƙwaya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Matsalolin Masarautun Kano Sun Kawo Karshe Najeriya
‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Cin Karensu Babu Babbaka A Najeriya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gangamin Wayar Da Kai Don Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Jihar Gombe Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shugaban Kasar Madagascar Ya Kori Prime Minista Da ‘Yan Majalisa Afrika
  • Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro Tsaro
  • Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kasashen Turai: Bazamu Yarda Da Dokar Harajin Trump Ba Labarai
  • Dakarun Zaman Lafiya Na Majalisar Dinkin Duniya Sun Rasa Rayukan Su Afrika
  • Ferfesa Pantami Yasamu Tikitin Takarar Gwamnan Gombe A Jami’yar PDP Afrika
  • Isra’ila Ta Cire Sunayen Wasu Mutane Biyu Cikin Wadanda Take Fako Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.