Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Kungiyar ISIS Ta Kashe Sojojin Amurka Biyu
Published: December 13, 2025 at 7:55 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

An kashe sojojin Amurka biyu da wani farar hula ba Amurke daya, yayin da aka raunata wasu mutanen uku a lokacin da wani dan kungiyar ISIS yayi musu kwanton bauna ya bude musu wuta a yankin tsakiyar kasar Sham, watau Syria a yau din nan.

Wannan shine harin farko da ya haddasa mutuwa da aka kai kan sojojin Amurka a kasar ta Sham tun daga lokacin da aka hambarar da gwamnatin Shugaba Bashar al Assad shekara guda da ta shige.

Rundunar sojojin Amurka a yankin gabas ta tsakiya ta ce domin mutunta ‘yan’uwan mamatan, ba zata bayyana sunayensu ba har sai bayan sa’oi 24 da sanar da su.

Sakataren tsaron Amurka, Pete Hegseth, ya rubuta a shafin X cewa duk wanda ya kai hari ya kashe Amurkawa a ko ina yake a duniya, zai shafe sauran ‘yan kwanaki kalilan da suka rage masa a duniya da sanin cewa Amurka zata farauto shi, ta hallaka shi.

Kamfanin dillancin labarai na kasar Sham, SANA, ya fada tun farko cewa wannan harin da aka kai a kusa da kangon birni mai tarihi na zamanin da da ake kira Tadmur, ko Palmyra a turance, yayi sanadin raunata wasu sojojin Sham guda biyu da wasu na Amurka da dama.

SANA yace an kashe maharin ba tare da ba da karin bayani ba amma kungiyar sa’ido kan al’amuran kare hakkin bil Adama a Sham mai hedkwata a Britaniya, ta ce maharin sojan kasar Sham ne.

Amurka tana da daruruwan sojojin da ta girka a gabashin kasar Sham a wani bangare na gamayyar yaki da ‘yan ISIS

Amurka

Post navigation

Previous Post: Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya
Next Post: Amurka Na Zargi Kasar Rwanda Da Kokarin Saba Yarjejeniyar Zaman Lafiya

Karin Labarai Masu Alaka

Jama’a A Yankin Gulf Sun Bukaci Dakatar Da Hare Hare Daga Washington Afrika
An Zargi Shugaba Trump Da Kalaman Da Basu Dace Ba Afrika
Dan Ra’ayin Mazan Jiya Leo Brent Zai Kyautata Alakar Afirka Ta Kudu Da Amurka Afrika
Amurka Da Isra’ila Sunkai Hari Kan Iran Amurka
Hukumomin Tsaron Najeriya Ne Suka Bukaci Amurka Ta Turo Musu Sojoji Amurka
‘Yan Sanda A Tsibirin Bahamas Sun kama Mijin Wata Ba Amurkiya Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar ICPC Ta Gayyaci Dangote Labarai
  • Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro Tsaro
  • Duk Da Rauni Daya Samu Sakamakon Hari Mojtaba Khameni Yafara Aiki Labarai
  • Ma’aikatan Tattara Kudin Haraji Sunyi Rikici Da Masu Babura A Bauchi Najeriya
  • ‘Yan Daba Sunkai Hari Kasuwar Waya A Kano Afrika
  • Kungiyar Kwadago Ta Shirya Zanga-Zanga A Najeriya Najeriya
  • Talauci Ya Ragu A Tsakanin Al’ummar Jihar Jigawa Siyasa
  • Bayan Shafe Shekaru Hudu A Mulki Sarkin Hausawan Ibadan Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.