Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Wani Bayahude Ya Harbe Bafalatsine Dan Shekaru 16
Published: December 17, 2025 at 8:30 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wani bayahude dan kama-wuri-zauna ya bindige wani Bafalatsine mai shekara 16 da haihuwa har lahira ranar talata a wani gari mai suna Tuqu dake yankin yammacin kogin Jordan, jim kadan a bayan da aka yi jana’izar wani matashin.

Yahudawa ‘yan kama wuri zauna sun kara yawan hare-haren da suke kaiwa kan Falasdinawa a yankin yammacin kogin Jordan tun bayan barkewar yaki a kan gaza, inda MDD ta fada cikin wani rahoto irin wadannan hare-hare sun yi muni zuwa adadin da ba a taba gani ba a watan oktoba.

Magajin garin na Tuqu, Mohammed al-Badan, ya fada ta wayar tarho cewa a bayan da aka yi jana’izar Ammar Sabah mai shekaru 16 wanda sojojin Isra’ila suka kashe, wani bayahude dan kama wuri zauna ya harbi wani matashin, shi ma mai shekara 16 da haihuwa, Muheeb Jibril, a kai, ya kuma kashe shi.

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Falasdinu ta ce sojojin Isra’ila sun kashe Sabah lokacin da suka kai farmaki ranar litinin a garin.

Akwai Falasdinawa kimanin miliyan biyu da dubu 700 dake zaune a yankin yammacin Kogin Jordan karkashin mamayar sojojin Isra’ila.

Isra’ila ta giggina garuruwa da unguwanni ma yahudawa a yankunan Falasdfinawan da ta kwace karfi da yaji sai dai akasarin kasashen duniya suna daukar wadannan matsugunan yahudawa a zaman na haramun, kuma akwai kudurori da yawa na Kwamitin Sulhun MDD da suka nemi Isra’ila da ta daina kakkaba irin wadannan garuruwan a yankunan na falasdinawa.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Lawal, Filin Wasa Na Rashidi Yekini Ko Turai Iyaka
Next Post: Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi

Karin Labarai Masu Alaka

An Bukaci Matasa Su Taka Gagarumar Rawa Wajen Gina Zaman Lafiya A Arewa Maso Gabas Afrika
Tinubu Ya Nuna Alhinin Rasuwar Janar Rabe Abubakar, Ya Jajanta wa Iyalansa Afrika
‘Yan Sanda A Tsibirin Bahamas Sun kama Mijin Wata Ba Amurkiya Amurka
Shugaba Tinubu Ya Bukaci Samar Da Zaman Lafiya A Filato Afrika
Shugaba Trump Yace Tehran Tana Neman Kulla Alaka Da Washington Amurka
Fargaba Ta Karu Duk Da Tsagaita Wuta Tsakanin Iran Da Amurka Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Bola Tinubu Ya Tafi Turai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Duk Da Rauni Daya Samu Sakamakon Hari Mojtaba Khameni Yafara Aiki Labarai
  • Ukraine Da Syria Zasuyi Haɗin Gwiwar Tsaro Labarai
  • Amurkawa Suna Turuwa Zuwa Kasar Faransa Duk Da Rashin Jituwa A Tsakanin Kasashen Amurka
  • Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida Afrika
  • Mutane Biyu Sun Mutu A Yayin Zaben Shugabannin Gundumomin APC A Jihar Ondo Najeriya
  • Afirka Ta Kudu Ta Samu Rigakafin Cutar Boro Afrika
  • Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.