Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Tinubu Ya Nada Shugabannin Hukumar NERC
Published: December 18, 2025 at 5:47 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Tinubu ya tabbatar da naɗin shugabannin Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC)

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da sake naɗa sabon kwamitin gudanarwa na Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC), biyo bayan tabbatar da su da Majalisar Dattawa ta yi a ranar 16 ga Disamba.

A cikin sanarwar da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar, an bayyana cewa Dokta Mulisiu Olalekan Oseni ne sabon Shugaban Hukumar (Chairman), Dokta Oseni, wanda ya fara aiki a NERC a matsayin Kwamishina tun watan Janairun 2017, daga bisani ya riƙe muƙamin Mataimakin Shugaba, Naɗinsa a matsayin Shugaba ya fara aiki ne daga 1 ga Disamba, 2025, kuma zai ci gaba har zuwa cikar wa’adin sa na shekaru goma, kamar yadda Dokar Wutar Lantarki ta 2023 ta tanada.

Haka kuma, Dokta Yusuf Ali ya zama Mataimakin Shugaban Hukumar (Vice Chairman) kuma An fara naɗa shi a matsayin Kwamishina a watan Fabrairun 2022, kuma sabon muƙaminsa zai fara aiki daga 1 ga Disamba, 2025, har zuwa ƙarshen wa’adinsa na farko.

Sauran mambobin kwamitin sun haɗa da Nathan Rogers Shatti da Dafe Akpeneye, waɗanda dukkansu ke kan wa’adin su na biyu bayan an fara naɗa su a watan Janairun 2017, Haka kuma, Aisha Mahmud Kanti Bello na ci gaba da wa’adinta na biyu, bayan an fara naɗa ta a watan Disambar 2020.

A ɓangaren sababbin mambobi, Dokta Chidi Ike na kan wa’adinsa na farko tun bayan naɗinsa a watan Fabrairun 2022, yayin da Dokta Fouad Animashaun ya fara wa’adinsa na farko daga Disamba, 2025. Dokta Animashaun ƙwararren masani ne a fannin tattalin arzikin makamashi, kuma ya taɓa zama Babban Kwamishina kuma Shugaban Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Jihar Legas.

Shugaba Tinubu ya buƙaci mambobin kwamitin NERC da su ƙara ƙaimi wajen zurfafa sauye-sauyen da ake yi a ɓangaren wutar lantarki a Nijeriya, tare da bin tanade-tanaden Dokar Wutar Lantarki ta 2023 gaba ɗaya.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Taron Sulhu Tsakanin Addinai Mabanbanta Na Arewacin Najeriya
Next Post: Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11

Karin Labarai Masu Alaka

An Kashe Mutane 25 Yayin Kai Wasu Hare Hare Jihar Adamawa Labarai
Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
Dalibai Sun Koma Makarantu A Wasu Jihohin Najeriya Najeriya
Shugaba Tinubu Ya Taya Musulmai Murnar Sallah, Tare Da Kira Zuwa Ga Kishin Kasa Afrika
Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai
Jam’iyyar APC Ta Rantsar Da Sabbin Shugabanni a Jihar Neja Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Tattalin Arzikin Kasar Botswana Zai Farfado Afrika
  • Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci Afrika
  • Kotun Amurka Tana Tuhumar Wani Dan Jarida Amurka
  • Sabon Jagoran Addinin Iran Mojtaba Khameni Yaji Rauni Kuma Ya Nakasa Afrika
  • Kotu A Kasar Uganda Ta Bada Belin ‘Yar Gwagwarmaya Afrika
  • Iran Zata Shigar Da Lebanon Cikin Cimma Yarjejeniya Afrika
  • Amurka Tayi Barazanar Rage Tallafinta Wa Sudan Ta Kudu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Magungunan Cutar Kolera Sun Makale A Dubai Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.