Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu
Published: December 19, 2025 at 11:21 AM | By: Yusuf Aliyu Harande

Rahotanni daga Jihar Nejan Najeriya na nuna cewa wata mace daga cikin mutane 17 da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su ta tutu a hannun ‘yanfashin dajin.

Tun a ranar 1/8/2025 ‘yanbindigar suka kutsa garin Ibeto a karamar Hukumar Magama suka kwashe mutane goma sha bakwai 14 daga cikin su matane sai kuma maza uku.

Masu garkuwar bukaci kudin fansa na naira milyan 150 kafin su sako wadan nan mutane, kuma har ya zuwa wannan lokaci mutanen garin na Ibeto basu hada wadannan kudaden ba.

Muhammad Kabir mazaunin garin na Ibeto yace tabbas sun samu labarin mutuwar daya daga cikin matan, sannan kuma wata matar guda da aka wuce da ita da ciki ta haihu a ranar Laraban nan da ta gabata.

Har yau dai babu wani bayani mai karfi daga bangaren gwamnatin Jihar Nejan akan kokarin karbo wadannan mutane na garin Ibeto,

Sai dai Shugaban karamar Hukumar ta Magama Dr. Muhmud Muhammad yace matsalar tana damunsu kuma cikin ikon Allah zasu samu mafita.

Kwamishinan Ma’aikatar kula da manyan Makarantun Jihar Nejan Farfesa Yakubu Auna, yace amatsayin su na masu ruwa da tsaki a yankin suna kokarin ganin an samu nasarar karbo wadannan mutane.

Mutuwar wannan baiwa Allah ta Ibeto a hannun ‘yanbindigar dai yana wuwa ne a dai dai lokacin da Kwamishina a hukumar Zabe ta jihar Neja Barista Ahmed Muhammad Borgu da Kuma tsohon shugaban Hukumar bada Ilimi bai daya ta jihar Nejan Hon. Alhasan Bawa Niworu suka share kimanin watanni uku a hannun ‘yanfashin da a yanzu haka bayanai ke nuna masu garkuwar sun bukaci milyan 300 kafin su sako su.

A yanzu dai hukumomin Jihar Nejan sun maida hankali wajan kokarin kubutar da sauran yara kimanin 200 da akayi garkuwa dasu a makarantar St Mary mallakar Cocin Katolica dake garin Papiri duk a Jihar Nejan.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/WATA-MATA-TA-MUTU-A-HANNUN-YANBINDIGA.mp3
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Tinubu: Ku Guji Yi Wadaka Da Kudin Kananan Hukumomi
Next Post: Rahoton MDD Yace An Kashe Fiye Da Farar 1000 A Sudan

Karin Labarai Masu Alaka

Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika
Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika
Sanata Sa’idu Alkali Ya Kaurace Wa Zaben Fidda Gwani Afrika
Gombe Ta Yi Fice A Duniya: Maryam Dan’azumi Ta Lashe Gasar Alƙur’ani Na Ƙasa Da Ƙasa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaban Amurka Donald Trump Yace Bai Taba Shiga Jirgin Jeffrey Epstein Ba Labarai
  • Kotun Amurka Ta Soke Harajin Fito Da Shugaba Trump Ya Kakabawa Kayan Kasashen Waje Amurka
  • Yaki Ta Sararin Samaniya Ya Cigaba Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Afrika
  • FIFA Na Shirin Fadada Babban Na’urar VAR A Gasar Cin Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • Isra’ila Takai Sabon Hari Tehran Ranar Lahadi Labarai
  • Jam’iyar SDP Tana Gudanar Da Babban Taro A Bauchi Afrika
  • An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali Tsaro
  • Akwai Shakku Akan Sanin Wacce Kungiyar Kwallon Kaface Zata Lashe Gasar Kofin Afirka Da Akeyi A Morocco Nishadi
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.