Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta
Published: December 23, 2025 at 8:34 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Rahotanni daga Afirka ta kudu suna kara bayyana yadda aka yaudari wasu ‘yan kasar suka tafi Rasha da sunan aikin tsaro ko makamancin haka, sai suka sami kansu a fagen daga a Ukraine, wani mahaifi Dubandlela yana cikin annashuwa da alfahiri lokacin da dansa dan shekaru 20 da haifuwa ya sanya hanu cikin watan Yulin bana, zai tafi Rasha inda za’a horas da jami’in tsaro da zai bada kariya ga masu hanu da shuni ko masu fada a ji.

Wata biyar bayan tafiyarsa, yanzu Dubandlela yana cike da takaici da zullumi, inda Dansa ya fada hanun mayaudara daga kungiyoyin sojojin haya, inda dansa da wasu akalla ‘yan kasar Afirka ta kudu 16 aka dauke su kuma aka tura fagen yaki a Ukraine.

Dubandlela yana aibunta kansa kan hali da dansa ya sami kansa a ciki, kuma Kakakin shugaban Afirka ta kudu Cyril Ramphosa, yace gwamnati tana “daukar batun da matukar muhimmanci.”

Yace kokarin kubutar da matasan yana da sarkakiya sosai, Kuma suna magana da dukkan sassan a yakin tsakanin Rasha da Ukraine, amma Vincent Magwenya yace sun fi bada karfi ne a magana da Rasha saboda an tura matasan ne ba shiri cikin rundunar mayakanta, Ya kara da cewa sun sami labari cewa matasan suna cikin hadari sosai a yankin Donbas.

Kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya fada, yaudarar da aka yi wa matasan ba zata rasa nasaba da zargin da aka yi wa ‘yar tsohon shugaban kasar Jacob Zuma, Lamari da ya tilasta mata yin murabus daga mjalaisar dokokin kasar.

Ma’aikatar harkokin wajen Rashar bata maida martani ba, da aka nemi jin ta bakinta a rubuce kan hanyoyin yaudarar matasan, da halinda suke ciki a halin yanzu

Afrika

Post navigation

Previous Post: Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka
Next Post: Asusun IMF Zai Bawa Kasar Misra Lamunin Sama Da Dala Biliyan 2

Karin Labarai Masu Alaka

Jirgin Hakar Mai Daga Turkiyya Ya Isa Mugadishu Afrika
Sojojin Da Suka Kifar Da Farar Hula A Guinea-Bissau Sun Sanar Da Cewa! Afrika
Shugaba Trump Ya Amince Da Tsawaita Cinikayya Tsakanin Amurka Da Kasashen Afirka Afrika
An Saka Dokar Hana Fita A Jos Ta Arewa Afrika
Babban Hafsan Tsaron Najeriya Ya Gargadi Jama’ar Arewa Maso Gabas Afrika
Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugabannin Kasashen Sahel Sunyi Taro a Mali Afrika
  • Shugaban Kasar Koriya Ta Arewa Ya Zamo Sakataren Jam’iya Mai Mulki Labarai
  • Gwamnatin Gombe Ta Raba Naira Miliyan 14 Ga Iyalen ‘Yan Jaridan Da Suka Rasu Najeriya
  • Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Zata Karbi ‘Yan Gudun Hijirar Da Amurka Ta kora Afrika
  • An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano Labarai
  • Iran: Za A Gudanar Da Jana’izar Khamenei Bayan Kwanaki Goma Na Muharram Afrika
  • Kasar China Ta Kaddamar Da Rawar Daji A Yankin Taiwan Labarai
  • An Kashe Mutane 169 A Wani Harin Sudan Ta Kudu Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.