Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Harin Makami Mai Linzami Da Rasha Ta Kai Yayi Barna Sosai A Ukraine
Published: December 23, 2025 at 8:57 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Hare-haren makamai masu linzami da jiragen drone da Rasha ta kai yau talata sun kashe mutane akalla uku cikinsu har da karamin yaro daya a Ukraine, tare da haddasa daukewar wutar lantarki a sassa da dama.

Wadannan hare-haren dake zuwa a bayan wani sabon zagaye na tattaunawar neman kawo karshen yakin na shekaru 4, sun fi lahani ga cibiyoyin samar da wutar lantarki na yammacin kasar.

Kasar Poland wadda ke makwabtaka da Ukraine a yamma, sai da ta tayar da jiragen saman yakinta a saboda hare-haren sun wakana dab da bakin iyakarta.

Shugaba Volodymyr Zelensky yace Rasha ta kai hare hare a kan yankuna akalla 13 na kasar.

Rasha ta ce ta kai hari a kan cibiyoyin samar da makamashi da na soji na Ukraine, ta kuma kama wasu kananan garuruwa biyu a bakin daga, amma ba a ji ta bakin kasar Ukraine kan wannan ba, kuma an san a baya tana musanta duk wani ikirarin Rasha na samun galaba a bakin daga.

Ita ma Ukraine ta kai nata harin cikin daren a kan wata masana’anta a yankin Stavropol na kudancin Rasha, ta haddasa tashin wuta a wurin a cewar gwamnan wannan yanki, Vladimir Vladimirov.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Shugaban Amurka Donald Trump Yace Bai Taba Shiga Jirgin Jeffrey Epstein Ba
Next Post: Sojin Ukraine Sun Janye Daga Gabashin Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Kudin Man Fetur Ya Karu Da Kashi 10 Cikin 100 Afrika
Ferfesa Pantami Yayi Watsi Da Amincewa Da Jamilu Isiyaku Gwamna Afrika
Hukumar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Jama’ar Jos Ta Arewa Su Rika Bin Doka Afrika
Shugaban Libya Ya Sayi Jirage Marasa Matuka Afrika
Gwamnatin Trump Tana Cigaba Da Korar Baki Daga Amurka Afrika
Hukumar Upper Benue Zata Inganta Noma A Dadinkowa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Shugaba Bola Tinubu Ya Amince Da Inganta Wutan Lantarki A Kasar Afrika
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
  • Akwai Bukatar Hukunci Mai Tsanani Ga Duk Wanda Yayi Fyade Najeriya
  • Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai
  • Muhawara Mai Zafi Tsakanin APC da ADC Shirye-Shirye
  • Tabbas Za’a Gudanar Da Gasar Firimiya Lig Ta Najeriya Wasanni
  • Najeriya: Ba Don Leken Asiri Muka Tura Jirgin Yakin Mu Ba Afrika
  • Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.