Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar
Published: December 24, 2025 at 2:27 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jamhuriyar Nijar ta kudiri aniyar rage yawan shinkafa da masara da alkamar da ke shiga kasar daga ketare da kashi 50% kafin nan da shekarar 2027.

Gwamnatin ta Nijar tace wannan wani mataki ne da ke hangen samar wa kasar cikeken ‘yancin kai a fannin cimaka a daidai lokacin da ta ke kokarin katse abin da ta kira ‘’ragowar igiyoyin mulkin mallaka’’ da a ke hasashen su na dabaibaye harakoki da dama.

Wakilin GTA Hausa Amurka ke Magana Souley Moumouni Barma ya aiko mana Cewar, Hekta 21200 ne gwamnatin ta Nijar ta ce ta dauri aniyar bajewa domin fadada aiyukan noman zamani ba’idin hekta 10000 da tuni aka riga aka ga tasirin da suka yi wajen samar da wadatar cimaka a kasar a cewar ministan noma da kiwo kanal Mahaman Alhaji Ousman a yayin da ya ke jawabi a zauren majalissar wakilai ta rikon kwarya CCR.

Ta hanyar wannan tsari da ake saran shimfidawa a jimilce kan hekta 39700 ana hasashen girbe amfani sau biyu a kowace shekara inji ministan wanda kuma ya kara da cewa abu ne da zai bada damar samun a kalla Ton 481000 na shinkafa daga nan zuwa shekarar 2027, lamarin da ka iya rage adadin shinkafar da ke shiga kasar daga waje har ma da marasa da alkama.

Bayanan ministan sun gamsar da ‘yan majalissar kamar su Issa Adam domin a ta su fahimta zartar da kudirin gwamnatin zai samar da sassaucin rayuwa a wajen al’umma.

Galibin jama’ar Nijar sun dogara kan noma da kiwo a matsayin hanyoyin samar wa kansu cimaka sai dai matsaloli masu nasaba da canjin yanayi na haifar da babban gibin amfani, a kowace shekara idan aka kwatanta da abinda ake samu a baya abinda ke zama silar tsadar farashi a kasuwanni.

Hakan yasa shugaban kungiyar kare hakkin masaya ta ADDC Maman Nouri ke yaba wa da shirin da hukumomin suka bullo da shi.

Dam dam da manyan madatsun ruwa ne ake shirin ginawa kari akan wadanda ake da su a baya domin tabbatar da wadatar ruwan da za a yi amfani da shi a aiyukan da aka sa gaba a illahirin jihohi, kamar yadda aka yi tanadin kwararrun ma’aikata da kayan aikin noman zamani a wani bangare na aiyukan da shugaban Nijar Janar Abdourahamane Tiani ya yi alkawali a kundin manufofinsa, aikin da zai lakume makuddan miliyoyin cfa.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Kotu A Birnin Tarayya Abuja Ta Bada Belin Tsohon Minista Abubakar Malami
Next Post: Jihar Kano Tayi Rashin ‘Yan Majalisu Biyu

Karin Labarai Masu Alaka

Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
Amurka Da Kasashen Yamma Suna Cigaba Da Kai Ruwa Rana Akan Nukiliyar Iran Afrika
Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya Afrika
Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika
GOSEMA Ta Horar Da Mambobin LEMCs A Jihar Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin Afrika
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ukraine Ta Aika Tawagar Kwararru Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Kano Pillars Ta Doke Ikorodu City Wasanni
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran Amurka
  • Gwamnatin Gombe: Babu Hannun mu a Cin Zarafin Kansilan Mazabar Shamaki Siyasa
  • Najeriya: Ba Don Leken Asiri Muka Tura Jirgin Yakin Mu Ba Afrika
  • Amurka Zata Fice Daga Iran Cikin Gaggawa Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.