Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar
Published: December 24, 2025 at 2:27 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Jamhuriyar Nijar ta kudiri aniyar rage yawan shinkafa da masara da alkamar da ke shiga kasar daga ketare da kashi 50% kafin nan da shekarar 2027.

Gwamnatin ta Nijar tace wannan wani mataki ne da ke hangen samar wa kasar cikeken ‘yancin kai a fannin cimaka a daidai lokacin da ta ke kokarin katse abin da ta kira ‘’ragowar igiyoyin mulkin mallaka’’ da a ke hasashen su na dabaibaye harakoki da dama.

Wakilin GTA Hausa Amurka ke Magana Souley Moumouni Barma ya aiko mana Cewar, Hekta 21200 ne gwamnatin ta Nijar ta ce ta dauri aniyar bajewa domin fadada aiyukan noman zamani ba’idin hekta 10000 da tuni aka riga aka ga tasirin da suka yi wajen samar da wadatar cimaka a kasar a cewar ministan noma da kiwo kanal Mahaman Alhaji Ousman a yayin da ya ke jawabi a zauren majalissar wakilai ta rikon kwarya CCR.

Ta hanyar wannan tsari da ake saran shimfidawa a jimilce kan hekta 39700 ana hasashen girbe amfani sau biyu a kowace shekara inji ministan wanda kuma ya kara da cewa abu ne da zai bada damar samun a kalla Ton 481000 na shinkafa daga nan zuwa shekarar 2027, lamarin da ka iya rage adadin shinkafar da ke shiga kasar daga waje har ma da marasa da alkama.

Bayanan ministan sun gamsar da ‘yan majalissar kamar su Issa Adam domin a ta su fahimta zartar da kudirin gwamnatin zai samar da sassaucin rayuwa a wajen al’umma.

Galibin jama’ar Nijar sun dogara kan noma da kiwo a matsayin hanyoyin samar wa kansu cimaka sai dai matsaloli masu nasaba da canjin yanayi na haifar da babban gibin amfani, a kowace shekara idan aka kwatanta da abinda ake samu a baya abinda ke zama silar tsadar farashi a kasuwanni.

Hakan yasa shugaban kungiyar kare hakkin masaya ta ADDC Maman Nouri ke yaba wa da shirin da hukumomin suka bullo da shi.

Dam dam da manyan madatsun ruwa ne ake shirin ginawa kari akan wadanda ake da su a baya domin tabbatar da wadatar ruwan da za a yi amfani da shi a aiyukan da aka sa gaba a illahirin jihohi, kamar yadda aka yi tanadin kwararrun ma’aikata da kayan aikin noman zamani a wani bangare na aiyukan da shugaban Nijar Janar Abdourahamane Tiani ya yi alkawali a kundin manufofinsa, aikin da zai lakume makuddan miliyoyin cfa.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Kotu A Birnin Tarayya Abuja Ta Bada Belin Tsohon Minista Abubakar Malami
Next Post: Jihar Kano Tayi Rashin ‘Yan Majalisu Biyu

Karin Labarai Masu Alaka

Muna Kira Ga Kasashen Duniya Su Sa Baki Don A Saki Mohamed Bazoum Afrika
Hukumar Zabe A Kasar Honduras Ta Sanar Da Nasry Asfura A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Shugaban Ƙasa Afrika
Rasha Da Ukraine Sun Cigaba Da Yakar Juna Afrika
‘Yan Sanda A Finland Sun Kwace Jirgin Ruwan Kasar Rasha Afrika
ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji Afrika
Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • FIFA, Ta Raba Jaddawalin Rukuni Na Gasar Kofin Duniya 2026. Wasanni
  • Gwamna Kefas Na Jihar Taraba Ya Karbi Shaidar Jam’iyar APC Siyasa
  • Janar Christopher Zai Maye Gurbin Ministan Tsaron Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa Labarai
  • An Samu Nasarar Karbo Karin Yara 130 Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu: Ku Guji Yi Wadaka Da Kudin Kananan Hukumomi Najeriya
  • Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
  • Tabbas Atiku Abubakar Ya Karbi Katin Jam’iyyar ADC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.