Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya!
Published: November 17, 2025 at 5:41 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 17, 2025

A wani harin da ‘yan-bindiga suka kai a cikin daren jiya Assabar, wayewar garin yau Lahadi a wata sakandaren ‘Yan Mata dake garin Maga wato (GGCSS Maga) a karamar hukumar Danko/Wasagu a jihar Kebbi Yan Bindigar sunyi garkuwa da Dalibai Mata 25 tare da kisan Mataimakin Shugaban Makarantar.
Al’umar garin Maga da  na Makarantar yanzu haka suna cikin firgici da damuwa sakamakon faruwar Lamarin.
Mazauna yankin sun ce maharan sun farwa makarantar ne da daddare, inda suka gudanar da aika-aikar su ba tare da wata ta gargada ba, kamar yada wata mazauniyar unguwar Murjanatu Hassan Gishiri ta bayyana lamarin a matsayin wani abin takaici da ya jefa daukacin masarautar Zuru cikin alhini.
Wani magidanci da ya zanta da gidan rediyon Amurka ke Magana yace an harbe mataimakin shugaban makarantar Malam Hassan Yakubu Makuku lokacin da yake kokarin kare daliban, yayinda wani ma’aikacin Makarantar Malam Ali Shehu, ya samu raunin harbin bindiga a hannu shi.
Rumdunar ‘Yan sandan jihar Kebbi a ta bakin mai magana da yawun ta CSP Nafi’u Abubakar ya tabbatar da faruwar Lamarin tare da bayyana cewa an sace dalibai 25 a yayin samamen.
A cewar rundunar ‘yan sandan, an tura tawagar hadin gwiwa ta rundunonin ‘yan sanda, da sojoji, da ‘yan banga domin binciken hanyoyin ‘yan bindigar a dazuzzukan da ke kusa da su da nufin ceto daliban tare da kamo maharan.
Kwamishinan ‘yan sanda Bello M. Sani ya tabbatar wa mazauna yankin kudurin hukumar na kare rayuka da dukiyoyi. Ya kuma bukaci jama’a da su kwantar da hankalinsu, su kuma lura, tare da tallafa wa ayyukan tsaro a yayin da ake ci gaba da bincike da ceto daliban.
Wasu mazauna yankin sun tabbatar da hakan a wata zanta da  suka yi da GTA Hausa, sun ce Jiragen Sojin Saman Najeriya na cigaba da shawagi a yankin, lamarin da ke nuna Dakarun Sojin sun fara aikin ceto Daliban.
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki
Next Post: An Yanke Hukuncin Kisa Ga Hasina Tsohuwar Firaiy-Ministan Bangladash

Karin Labarai Masu Alaka

Najeriya: Ta Aiwatar Da Tsarin Ba Aiki Ba Albashi Ga Ma’aikata Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
2025 Ta Bar Baya Da Abubuwa Masu Ban Al’ajabi, 2026 Barka Da Zuwa! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Zamu Hana Wasu ‘Yan-Najeriya Visa Shiga Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Aliko Dangote: Faruk Ahmed Ya Ci Amanar ‘Yan Najeriya! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Yanbindiga sun Kashe kimanin mutane 30 a yankin kayama ta Jihar kwaran Najeriya Najeriya
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Tace A Maboyar ‘Yan Ta’adda Aka Kai Harin Jilli Afrika
  • Shugaba Tinubu Ya Kara Aika Sunayen Jakadu Ga Majalisa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zamu Hana Wasu ‘Yan-Najeriya Visa Shiga Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria Siyasa
  • Libya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasashen Faransa Da Amurka Afrika
  • Farashin Mai Yayi Tashin Gwaron Zabi Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.