Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An Kashe Mutum 2 Da Suka Ba ‘Yan-Matan (GGCSS Maga) Kariya!
Published: November 17, 2025 at 5:41 PM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: November 17, 2025

A wani harin da ‘yan-bindiga suka kai a cikin daren jiya Assabar, wayewar garin yau Lahadi a wata sakandaren ‘Yan Mata dake garin Maga wato (GGCSS Maga) a karamar hukumar Danko/Wasagu a jihar Kebbi Yan Bindigar sunyi garkuwa da Dalibai Mata 25 tare da kisan Mataimakin Shugaban Makarantar.
Al’umar garin Maga da  na Makarantar yanzu haka suna cikin firgici da damuwa sakamakon faruwar Lamarin.
Mazauna yankin sun ce maharan sun farwa makarantar ne da daddare, inda suka gudanar da aika-aikar su ba tare da wata ta gargada ba, kamar yada wata mazauniyar unguwar Murjanatu Hassan Gishiri ta bayyana lamarin a matsayin wani abin takaici da ya jefa daukacin masarautar Zuru cikin alhini.
Wani magidanci da ya zanta da gidan rediyon Amurka ke Magana yace an harbe mataimakin shugaban makarantar Malam Hassan Yakubu Makuku lokacin da yake kokarin kare daliban, yayinda wani ma’aikacin Makarantar Malam Ali Shehu, ya samu raunin harbin bindiga a hannu shi.
Rumdunar ‘Yan sandan jihar Kebbi a ta bakin mai magana da yawun ta CSP Nafi’u Abubakar ya tabbatar da faruwar Lamarin tare da bayyana cewa an sace dalibai 25 a yayin samamen.
A cewar rundunar ‘yan sandan, an tura tawagar hadin gwiwa ta rundunonin ‘yan sanda, da sojoji, da ‘yan banga domin binciken hanyoyin ‘yan bindigar a dazuzzukan da ke kusa da su da nufin ceto daliban tare da kamo maharan.
Kwamishinan ‘yan sanda Bello M. Sani ya tabbatar wa mazauna yankin kudurin hukumar na kare rayuka da dukiyoyi. Ya kuma bukaci jama’a da su kwantar da hankalinsu, su kuma lura, tare da tallafa wa ayyukan tsaro a yayin da ake ci gaba da bincike da ceto daliban.
Wasu mazauna yankin sun tabbatar da hakan a wata zanta da  suka yi da GTA Hausa, sun ce Jiragen Sojin Saman Najeriya na cigaba da shawagi a yankin, lamarin da ke nuna Dakarun Sojin sun fara aikin ceto Daliban.
Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki
Next Post: An Yanke Hukuncin Kisa Ga Hasina Tsohuwar Firaiy-Ministan Bangladash

Karin Labarai Masu Alaka

Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Amurka Ta Yi Juyin Mulki A Kasar Venezuela Amurka
Farashin Dalar Amurka Ya Tashi Ranan Juma’a Amurka
Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
An Fara Azumin Watan Ramadan A Najeriya Da Sassan Duniya  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Amurka Da Iran Zasu Tattauna A Kasar Oman Amurka
  • Shugaba Trump Yace Bazai Bari Iran Ta Mallaki Nukiliya Ba Amurka
  • Majalisar Dattawan Amurka Ta Amince Da Wata Doka Amurka
  • Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno Tsaro
  • Magoya Bayan Dan Hamayya A Afirka Ta Kudu Sun Hallara A Kotu Afrika
  • Madrid, Arsenal Da Chelsea Sun Fara Zaurancen Dan-Wasa Kenan Yildiz Wasanni
  • Salmanu: Ci Gaban Wikki Tourist FC Shine A Gaba Na Wasanni
  • An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.