Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Rundunar Operation Hadinkai Sunyi Nasara Akan ISWAP Da Boko Haram
Published: January 12, 2026 at 12:45 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Dakarun Operation Hadin Kai (OPHK) sun ƙara zafafa hare-haren su kan mayakan Boko Haram da ISWAP a jihar Borno, wanda ya haifar da gagarumar nasara a yaki da ta’addanci.

A cewar sanarwar da jami’in hulɗa da manema labarai na Rundunar Haɗin Gwiwa a Arewa Maso Gabas, Laftanal Kanar Sani Uba ya fitar, dakarun sun tilasta wa ‘yan ta’adda 11 su miƙa wuƙa a yankin Azir–Wajiroko tare da mayar da AK-47 da harsasai daban-daban.

A ranar 9 ga Janairu, 2026, dakarun sun gudanar da gagarumin farmaki a yankin Bula-galda, inda suka lalata sansanonin ‘yan ta’adda a Dagumba, Bonne, Yaganari, Gosuri da Umchile, kuma lokacin farmakin, an rusa mafaka da dama, an katse hanyoyin samar musu da kayan aiki, kuma an kwato tutocin ta’addanci, bindigogi da makamai.

A wasu farmakin da suka gudana a yankunan Yale da Bula Gaida, sojojin sun sake rusa cibiyoyin kayan aiki na ‘yan ta’adda, tare da kwato bindigogi, harsasai da bindigar gurneti.

Haka kuma, bisa sahihan bayanan leƙen asiri, dakarun sun fafata da mayaƙan JAS/ISWAP a tsakanin kauyukan Sojiri da Kayamla, inda suka kashe ‘yan ta’adda 8.
An kuma kama wasu mutane biyu da ake zargin suna ba da kayan aiki ga ‘yan ta’adda a ƙaramar hukumar Gubio.

Rundunar Sojojin Najeriya ta jaddada kudirinta na dawo da zaman lafiya a Arewa maso Gabas tare da roƙon al’umma da su ci gaba da ba da sahihan bayanai don taimaka musu a yaki da ta’addanci.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Barcelona Ta Lashe Kofin Spanish Super Cup 
Next Post: Manchester United: Za Ta Nada Michael Carrick A Matsayin Kocin Riƙon ƙwarya

Karin Labarai Masu Alaka

Burkina Faso Ta Sako Jami’an Rundunar Sojin Saman Najeriya 11 Da Aka Tsare Tsaro
Hawan Sallah A Jihar Katsina Afrika
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Aikin Wutan Lantarki A Jami’ar Bayero Afrika
Kamfanin Dangote Zai Sayo Na’urori Daga Kasar China Kimiya
Usman Maiyama Ne Gwarzon Kamun Kifin Argungu Bana Labarai
Masu Ruwa da Tsaki akan Lamurran Siyasa sun Fara Maida Martani akan Matakin da Ministan Labaran Nigeria da wayar da kan Jama,a Idris Malagi na korar Daya Daga cikin Ma,aikatansa Saboda dalilai na Siyasa. da tsakiayar ranar Wannan larabace dai Mataimakin na Musamman akan yada Labarai ga Minista Malagi Malam Rani,u Ibrahim ya fitar da Wata sanarwar cewa Ministan ya Dakatar da Daya Daga cikin Ma,aikatansa Mai Suna Sa,idu Enagi Saboda ya fitar da Wani bayani a Kafar yada Labarai na sada zumunta dake Nuna Ministan ya shirya tsaf Domin takarar Gwamnan Jihar Neja a 2027. Malam Sa,idu Etsu Tsohon Dantakarar Shugaban cin Jam,iyyar APC a Nigeria Yace Matakin da Ministan ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu lokaci baiyi ba..ceu.. Shima Dattijon Siyasa a Jihar Neja Alh.Awaisu Giwa Kuta Yace Matakin da Ministan Labaran ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu Jihar Neja zaman Makoki Ake na fotinar Yan ta,adda ba wai Batun Neman Mukamin Siyasa ba..ceu .in.. To Sai jigon Jam,iyyar PDP Mai Adawa a Nigeria Hon.Yahaya Ability Yace Akwai kuskure Babba da Ministan ya tabka a dai dai Wannan Zamani na Siyasa duk da cewa Jihar Nejan na cikin Yanayi na masifar Yanbindiga..ceu..in .. Azaben Shekara ta 2023 Malagi ya kara yayi Takara Gwamnan Jihar Neja a jam,iyyar APC inda Gwamna Umar Bago ya kadashi a zaben fidda Gwani. Martanin Wasu ‘Yan Najeriya Ga Ministan Labarai Bisa Korar Dadiminsa Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar Zabe A Kasar Honduras Ta Sanar Da Nasry Asfura A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Shugaban Ƙasa Afrika
  • ‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Magajin Garin Istanbul Dake Kurkuku Ya Bukaci A Gudanar Da Zabe Labarai
  • Hukumomin Taliban Sunce A Shirye Suke Domin Sulhu Afrika
  • An Gudanar Da Zanga-Zanga A Kasar Somaliya Labarai
  • Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta Afrika
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe  Afrika
  • Malami: Gwamnatin APC Ta Gaza – “Yan-Kasa Kuwa Na Da Katin Zabe” Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.