Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

‘Yan Ta’adda Sun Tarwatsa Wani Kauye A Jihar Sakkwato
Published: January 17, 2026 at 10:16 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 18, 2026

Mutane na ci gaba da tserewa daga gidajen su a kauyukan da ke jihar Sokoto sakamakon barazanar da ‘yan ta’adda suke musu.

Al’ummar karamar hukumar Isa sun koka kan yadda hare-haren ‘yan ta’addar yayi tsamari, tun bayan da shugaban wata kungiyar ‘yan ta’adda ya yi barazanar hallaka mazauna kauyen Tidibali, da yake zargin sun yi musu shune wajen jami’an tsaro, idan basu bar garin ba, ranar Jumu’ar da ta gabata.

Bello Turji ya far wa Tidibali, inda ya kashe mutane 3, kuma yayi gargadin idan ya sake dawowa kowaye ya tarar zai shaki lahira, don ko kaza ba zai bari ba.

Mazauna yankin sun ce wasu daga cikin ‘yan uwan su na tserewa kasar Nijar, ta bin hanyoyi masu matukar hatsari don su tsira da rayukan su.

Mutane da dama sun tsere zuwa kasar Nijar a cewar mazauna yankin, inda wasu suka kwashe iyalan su kaf, har da iyaye. Amma akwai wadanda sukai rashin sa’a, hukumomin Nijar suka kama su suka dawo da su Nigeria.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Mutane Da Dama Sun Rasa Rayukansu Yayin Rikici A Uganda
Next Post: Trump Zai Sasanta Tsakanin Masar Da Habasha

Karin Labarai Masu Alaka

Rwanda Zata Janye Dakaru Daga Mozambique Afrika
Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno Afrika
Kasashe Biyar Zasu Tura Sojoji Domin Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya A Gaza Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Gurfaranar Da Wadanda Ake Zargi Takai Hari Gaban Kotu Najeriya
Iran Zata Kai Hari Tashar Makamashin Ruwa A Gulf Afrika
Hukumar Ƴan Sanda Ta Musanta Zargin Kashe Ɗan Achaba a Gombe Tsaro

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Jirage Marasa Matuka Sun Kaiwa Jiragen Ruwan Mai Hari A Gulf Afrika
  • Dalibai Sun Koma Makarantu A Wasu Jihohin Najeriya Najeriya
  • Manoma Suna Fuskantar Barazanar Karyewa A Kasar Ghana Afrika
  • Shugaban Amurka Zai Sake Aika Jirgin Yaki Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Majalisar Dokokin Kamaru Ta Amince Da Wasu Sauye Sauye Afrika
  • Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar Afrika
  • Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno Afrika
  • Kungiyoyin Fararen Hula A Gombe Sun Bukaci A Bawa Mata Jagoranci Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.